An rufe wasu makarantu a yankunan Nyanya da ke Abuja da kuma Mararaba da ke Jihar Nasarawa a ranar Alhamis, bayan samun rahoton barazanar tsaro da ya jawo fargaba tsakanin iyaye da hukumomin makarantu.
A Mararaba, musamman a yankunan Aso A da Aso B, makarantu sun dakatar da karatu, yayin da iyaye suka riƙa garzayawa domin ɗaukar ‘ya’yansu daga makaranta.
Wasu makarantu kamar Henjodan Primary and Secondary School da Merit Gate Scholar Academy sun sallami ɗalibai da wuri saboda fargaba.
Fargabar ta biyo bayan jita-jitar cewa an kai hari wata makaranta a Nyanya inda ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai hari.
Wani ɗalibi ya ce an umarce su da su koma gida bayan labarin ya fara yawo a gari.
“An ce akwai wani abu da ya faru a Nyanya, shi ya sa aka ce mu koma gida,” in ji ɗalibin.
Sai dai har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, babu wata sanarwa a hukumance da ta tabbatar da cewa an kai hari ko an yi garkuwa da ɗalibai a yankin.
‘Yansanda sun riga sun ƙaryata rahoton sace ɗalibai a Nyanya, inda suka ce ana ci gaba da bincike domin gano gaskiyar abin da ya faru.
Hukumomi da jami’an tsaro har yanzu ba su fitar da cikakken bayani ba game da lamarin.















Discussion about this post