Ma’aikatar harkokin wajen Sin ta ce shugaba Xi Jinping da takwaransa na Rasha Vladimir Putin, za su yi musayar ra’ayi kan dangantakar kasashensu da hadin gwiwa a fanoni daban-daban da batutuwan yanki da na duniya da ke jan hankalinsu, a yayin ziyarar da Putin zai kawo kasar Sin a gobe Talata.
Yayin taron manema labarai na yau Litinin, kakakin ma’aikatar Guo Jiakun, ya ce bisa gayyatar shugaba Xi, Vladimir Putin zai ziyarci Sin daga gobe Talata 19 zuwa Laraba 20 ga wata, kuma wannan za ta kasance ziyara ta 25 da Putin zai yi a Sin.
A cewar kakakin, kasashen biyu za su dauki ziyarar a matsayin wata dama ta inganta dangantakar Sin da Rasha zuwa sabon mataki, da kara wa duniya kuzari da kwanciyar hankali. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post