ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Arewa Za Ta Fi Ko Ina Cin Moriyar Sauye-sauyen Da Na Ke Yi – Tinubu

by Sadiq
1 week ago

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya ce Arewacin Nijeriya ne zai fi amfana da sauye-sauyen tattalin arziƙin gwamnatinsa ke yi, musamman cire tallafin man fetur.

Tinubu ya ce sauye-sauyen sun taimaka wajen karkatar da kuɗaɗen gwamnati zuwa ayyukan more rayuwa, ilimi da sauran fannoni masu amfani.

Da yake magana ta hannun Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Nentawe Yilwatda, a wani taron manufofin jam’iyyar da aka gudanar a Abuja, shugaban ya ce ayyuka kamar bututun iskar gas na Ajaokuta-Kaduna-Kano, NELFUND da manyan ayyukan tituna za su samar da ƙarin damar tattalin arziƙi a Arewa.

ADVERTISEMENT

Tinubu ya ce, “Arewa ce za ta fi amfana da wannan tattalin arziƙi,” yana mai cewa yankin zai samu damar cinikayya da maƙwabtan ƙasashe.

Shugaban ya kuma kare matakin cire tallafin man fetur, yana mai cewa duk da wahalar da matakin ya haifar, ya zama dole domin ceto ƙasar daga ƙarin matsaloli.

LABARAI MASU NASABA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

Sai dai ƙungiyoyin Arewa Consultative Forum (ACF) da Middle Belt Forum (MBF) sun yi watsi da iƙirarin shugaban.

ACF ta bayyana kalaman a matsayin abin mamaki, tana mai cewa ƙaruwar talauci, rashin tsaro, ƙarancin ababen more rayuwa da matsalolin noma na nuna cewa har yanzu ’yan Arewa da dama na fama da matsaloli.

MBF ma ta ce cire tallafin man fetur ya shafi ’yan Nijeriya a faɗin ƙasar, don haka bai kamata a bayyana shi a matsayin manufar da ta fi amfanar da wani yanki ba.

A gefe guda, jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta ce za ta dawo da tallafin man fetur idan ta lashe zaɓen 2027.

Jam’iyyar ta ce hakan zai taimaka wajen rage tsadar rayuwa.

Sai dai wasu shugabannin Kiristocin Arewa suna da saɓanin ra’ayi da masu sukar gwamnatin Tinubu, inda suka ce Arewa ta amfana da ayyukan gwamnati a fannonin tituna, ilimi da lafiya.

Rev. John Hayab ya ce Tinubu ya fi tsohon Shugaban Ƙasa marigayi Muhammadu Buhari yin aiki, yana mai kira ga ’yan Arewa da su amince da ayyukan da aka gudanar tare da ci gaba da neman gwamnati ta yi ƙarin wasu.

Sai dai ya amince cewa rashin tsaro, talauci da yunwa manyan matsaloli ne da har yanzu ke addabar yankin Arewa.

MASU ALAKA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
Manyan Labarai

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Next Post
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.