Arziƙin hamshaƙin attajirin Afirka, Aliko Dangote, ya haura dala biliyan 50 bayan fara sayar da hannayen jarin matatar man fetur ɗinsa.
Mujallar Forbes ta ce arziƙin Dangote ya ƙaru da kusan dala biliyan 20, sakamakon fara sayar da hannayen jarin matatar, wadda ita ce mafi girma a Afirka.
Dangote, wanda shi ne mutum mafi arziƙi a Afirka, ya fara bai wa jama’a damar mallakar hannayen jarin matatar a ranar Litinin, 14 ga watan Satumba.
Kamfanin zai sayar da hannayen jari biliyan 4.1, wanda ya kai kashi 3.3 cikin 100 na kamfanin, a farashin Naira 525 kan kowane hannun jari.
Mafi ƙarancin hannayen jarin da mutum zai iya saya shi ne 10, yayin da za a rufe buƙatar sayen hannayen jarin a ranar 13 ga watan Oktoba.
Ana sa ran fara sayar da hannayen jarin Matatar Dangote a Kasuwar Hannayen Jari ta Nijeriya a watan Nuwamba.
Dangote ya ce dalilin fara sayar da hannayen jarin shi ne bai wa jama’a damar mallakar wani kaso na matatar tare da samun damar cin moriyar arziƙinta.
Ya bayyana sayar da hannun jarin a matsayin wani muhimmin mataki ga kamfanin da kuma masu zuba hannayen jari.














