Shugaban Rukunin Kamfanonin Dangote, Aliko Dangote, ya buƙaci ’yan Nijeriya da sauran ’yan Afirka su zuba jari a hannayen jarin matatarsa, inda ya bayyana cewa za su samu riba mai yawa da kuma arziƙi na tsawon lokaci.
Da yake magana a wajen ƙaddamar da shirin sayar da hannayen jarin a Kasuwar Hannayen Jarin Nijeriya (NGX) da ke Legas, Dangote ya ce tayin dala biliyan 1.6 shi ne mafi girma da aka taɓa gudanarwa a kasuwar hannayen jari a Afirka.
Kamfanin zai sayar da hannayen jari biliyan 4.1, kan farashin Naira 525 ga kowanne, yayin da mafi ƙarancin abin da mutum zai iya saya shi ne hannaye 10, wanda darajarsu ta kai Naira 5,250.
Dangote ya ce matatar ta samu gagarumar nasara ta fuskar kuɗi, inda ta samu kuɗin shiga kusan Naira tiriliyan 19.47, sannan ribar da ta samu bayan cire haraji ta kai Naira tiriliyan 2.55 cikin watanni shida na farkon shekarar 2026.
Ya ce masu zuba jari za su iya samun riba ta hanyar raba wa kowa kasonsa da kuma ƙarin darajar hannayen jarin matatar a nan gaba.
Ya ƙara da cewa shirin zai bai wa miliyoyin ’yan Nijeriya damar zama masu hannun jari a ɗaya daga cikin manyan masana’antun Afirka.














