Wakiliyar Asusun Yara na MDD wato UNICEF Amakobe Sande, ta bayyana yadda kasar Sin ta cimma manyan nasarori a fannin kyautata tsarin bayar da hidima ga yara masu bukata ta musamman.
Malama Sande, ta bayyana haka ne gabanin bikin ranar yara ta duniya, inda ta kara da cewa, yadda kasar Sin ta fitar da doka, da manufar kafa muhallin da mutane masu bukata ta musamman ke iya rayuwa ba tare da wata matsala ba, ya kasance muhimmin mataki na raya ayyukan bayar da hidima ga mutane masu bukata ta musamman.
Haka zalika, ta ce kasar Sin ta yi ta bayar da karin taimako ga iyalan dake da yara masu bukata ta musamman, bisa kwaskwarimar da kasar ta yi a fannin bayar da tallafi ga yara.
A sa’i daya kuma, yara masu bukata ta musamman a kasar Sin, suna iya shiga makarantu na yau da kullum, bisa manufar hadin gwiwar aikin ba da ilmi da kasar ta kaddamar.
Tun daga karshen shekarar 2022, Asusun UNICEF ke hada kai da hukumomin bayar da ilmi ta kasar Sin, wajen aiwatar da shirin ba da ilmi na hadin gwiwa.
Kana ya zuwa shekarar 2025, an aiwatar da wannan shiri a makarantun firamare da sakandare, har ma da gidajen renon yara da yawansu ya kai 1,682, a larduna 7 dake fadin kasar Sin, lamarin da ya bayar da tallafi ga yara kimanin miliyan 1 da dubu 100. (Mai Fassara: Maryam Yang)















Discussion about this post