Ƙungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) reshen Jami’ar Jos (UNIJOS) ta dakatar da yajin aikin da ta fara bayan an biya malaman albashin watan Maris na shekarar 2026.
Ƙungiyar ta fara yajin aikin ne a ranar Laraba sakamakon jinkirin biyan albashi da kuma rashin biyan kuɗaɗen alawus-alawus na malamai (EAA).
- Jimillar Darajar Kayayyakin Da Ake Samarwa a Cibiyoyin Fasaha Na Kasar Sin a 2025 Ta Zarce Yuan Tiriliyan 20
- Fulham Na Duba Yiwuwar Daukar Chukwueze Na Dindindin
A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Juma’a, shugaban ASUU na UNIJOS, Jurbe Molwus, ya tabbatar da cewa mambobin ƙungiyar sun fara jin alat na biyan albashi, lamarin da ya sa suka yanke shawarar dakatar da yajin aikin, duk da cewa har yanzu ba a biya kuɗaɗen EAA ba.
“Mun samu bayani cewa, hukumar jami’ar ta samu amincewa daga Ofishin Babban Akanta na Tarayya, domin biyan albashin watan Maris, ‘yan sa’o’i bayan mun fara yajin aiki a ranar 8 ga Afrilu, 2026,” in ji sanarwar.
Molwus ya bayyana cewa, ƙungiyar ta tabbatar da biyan albashin a dukkan sassan jami’ar kafin ta yanke hukuncin janye yajin aikin.















Discussion about this post