Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC a zaɓen 2027, Atiku Abubakar, ya soki hukuncin kotu da ta yanke na bayar da umarnin soke rajistar jam’iyyar da wasu jam’iyyun hamayya.
Kotun ta ba da umarnin soke rajistar jam’iyyar ADC da wasu jam’iyyun hamayya guda huɗu.
Atiku ya bayyana hukuncin a matsayin yi wa tsarin dimokraɗiyyar Nijeriya kisan mummuƙe da kuma ƙoƙarin raunana jam’iyyun hamayya gabanin babban zaɓen shekarar 2027.
A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin, Atiku ya bayyana cewa alƙalin ya yi kunnen uwar shegu da umarnin da Babbar Kotun Ɗaukaka Ƙara ta bayar tun da fari na dakatar da duk wani mataki kan shari’ar.
Ya yi gargaɗin cewa watsar da umarnin kotu yana jefa al’amura cikin hatsari.
Haka kuma, Atiku ya zargi gwamnatin Shugaba Tinubu da mayar da hankali wajen ganin bayan abokan hamayyarta na siyasa, maimakon ta magance manyan matsalolin da ke damun ƙasa kamar talauci, rashin aikin yi, da kuma rashin tsaro.
Duk da wannan hukunci, Atiku ya yi kira ga magoya bayansa da su kwantar da hankalinsu.
Ya yi alƙawarin cewa jam’iyyar ADC za ta bi hanyoyin shari’a don ƙalubalantar wannan mataki, inda ya bayyana lamarin a matsayin “yaƙi domin ceto dimokraɗiyyar Nijeriya.”















Discussion about this post