Dakarun Sojin tare da haɗin gwiwar sojin sama sun ceto Hajiya Amina Abubakar, matar tsohon Kakakin Rundunar, Manjo Janar Rabe Abubakar, bayan ‘yan bindiga sun sace ta tare da mijinta a Jihar Katsina makonni biyu da suka wuce.
Hukumar tsaro ta ce an gudanar da aikin ceto ne a ƙarƙashin Operation FASAN YAMMA, inda sojoji suka kai farmaki kan ‘yan bindigar a ƙauyen Tunga, lamarin da ya tilasta musu tserewa.
A yayin arangamar, ‘yan bindigar sun harbe ta kafin su tsere, amma sojoji sun ceto ta tare da garzaya da ita zuwa asibitin sojoji, inda take karɓar magani kuma tana samun sauƙi.
Sojojin sun ce za su ci gaba da farautar maharan domin kawar da ‘yan bindiga daga yankunan Katsina da sauran sassan ƙasar.
idan ba a manta ba mijinta ya rasu a hannun maharan da suka sace shi, inda gwamnatin Katsina ta ce ya rasu sakamakon fama da ciwon suga da hawan jini.
Amma iyalan marigayn sun ce wannan bayani ba gaskiya ba ne, domin mahaifinsu ba shi da ciwon suga bare hawan jini.
Sun danganta rasuwar mahaifinsu da cizon maciji da ya samu a hannun waɗanda suka sace shi tare da matarsa.














Discussion about this post