• English
  • Business News
Tuesday, July 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba A Yabon Dan Kuturu…

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ba A Yabon Dan Kuturu…
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daga ranar 18 zuwa 19 ga wannan wata ne, sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya kawo ziyara kasar Sin, ziyarar da masana suka ce tana da babbar ma’ana duk da cewa, yanzu dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka ta gamu da matsala mafi tsanani, tun bayan da kasashen biyu suka kulla dangantakar diflomasiyya a tsakaninsu, wanda bai dace da moriyar jama’ar kasashen biyu da ma begen da kasa da kasa ke yi ba.

Sin dai tana kokarin raya dangantakar dake tsakaninta da kasar Amurka cikin lumana da yadda hakan zai amfanawa duniya baki daya.

  • Sin Na Son Yin Hadin Gwiwa Da Dukkan Bangarori Don Inganta Ci Gaban Da Aka Samu Na Dogon Lokaci Na Hadin Gwiwar Ayyukan Raya Kasa Da Kasa

Kana tana fatan kasar Amurka za ta fahimce ta bisa hakikanin yanayi, da yin kokari tare da kasar Sin din, wajen tabbatar da tushen siyasa na raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, da daidaita matsaloli yadda ya kamata, da kokarin aiwatar da shawarwarin da shugabannin kasashen biyu suka cimma a tsibirin Bali, da sa kaimi ga maido da dangantakarsu bisa turbar da ta dace.

Bangaren Amurka dai ya sha alkawarin mutunta alkaruwan da sassan biyu suka cimma a lokuta da matakai daban-daban don inganta alakar sassan biyu, amma sai a wayi gari Amurka ta sake mayar da hannun agogo baya.

A jawabinsa yayin ganawa da shugabannin Sin yayin ziyararsa a Beijing, Blinken ya bayyana cewa, Amurka na mutunta alkawuran da shugabannin kasashen suka ya yi, kuma Amurka ba ta neman “sabon yakin cacar baka”, ba ta neman sauya tsarin kasar Sin, ba ta neman adawa da kasar Sin ta hanyar karfafa kawance, kana ba ta goyon bayan ‘yancin kai na yankin Taiwan”. Amurka ba ta da niyyar yin rikici da kasar Sin, kuma tana fatan yin mu’amala mai zurfi tsakanin manyan jami’anta da kasar Sin, da kiyaye hanyoyin tattaunawa marasa shinge, da warware bambance-bambancen dake tsakaninsu, da neman tattaunawa, da yin musaya da hadin gwiwa. Sai dai masu iya magana na cewa, ba a yabon dan kuturu sai ya shekara da yatsa. Ma’ana sai mun ga Amurka ta cika wadannan kalamai da ta fada.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Hanya mafi dacewa ta warware batutuwa da suka shafi kasa da kasa, ita ce tattaunawa, maimakon ware kai, da mayar da wasu saniyar ware, da yin komai a bayyane, da damawa da kowa da kowa, tare da ci gaba da shawarwari da yin hadin gwiwa, maimakon yin fito na fito.

Haka kuma, ya dace a rika martaba zabin kasashe na samun bunkasuwa, maimakon fakewa da wani batu na siyasa ko wata manufa da nufin cimma wata moriya ko neman tayar da fitina a sauran kasashe.

Sanin kowa ne cewa, takarar manyan kasashen duniya ba ta wakiltar yanayin da ake ciki, kuma hakan ba zai taba iya magance matsalolin Amurka ko kuma kalubalen da duniya ke fuskanta ba.

Sannan bai dace wani bangare ya yi kokarin siffanta daya bangaren bisa son ransa, sannan ya hana daya bangaren hakkinsa na samun ci gaba ba. Abin jira a gani dai shi ne, ko Amurka za ta cika alkawuranta? Kyawun alkawari dai aka ce cikawa. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kroos Ya Kara Kwantiragin Shekara 1 A Real Madrid

Next Post

Kai Harvertz Ya Koma Arsenal Daga Chelsea

Related

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

50 minutes ago
Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

3 hours ago
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

3 hours ago
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%
Daga Birnin Sin

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

4 hours ago
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

5 hours ago
Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro
Daga Birnin Sin

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

6 hours ago
Next Post
Kai Harvertz Ya Koma Arsenal Daga Chelsea

Kai Harvertz Ya Koma Arsenal Daga Chelsea

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

July 15, 2025
Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 15, 2025
VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

July 15, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

July 15, 2025
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

July 15, 2025
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

July 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

July 15, 2025
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

July 15, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

July 15, 2025
Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

July 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.