ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

by Idris Aliyu Daudawa
49 minutes ago
Kano

Jihar Kano ta kasance  jagora da aka ɗauke ta wadda ta ke yin abubuwa ko ayyukan da suka shafi  gwamnati a ƙungiyar ƙawancen tattalin arziki kan kashe kuɗin domin lamarin da ya shafi ilimi kamar dai yadda rahoton da Jami’ar Paris ta wallafa na shekarar 2026.

Rahoton ya bayyana Kano ta ɗaya daga cikin gwamnatoci 209 waɗanda suke daga ƙasashe 15 da suke ƴan ƙungiyar ne, inda aka bada misali da Jihar kan yadda take ci gaba da zuba jari sai kuma aiwatar da ayyuka kamar yadda suke a cikin kasafin kuɗi na ilimi.

Yadda Jihar Kanon ta kasance ta ɗaya ya biyo bayan ganin yadda ta bayyana aniyarta ta kafa dokar ta ɓaci kan lamarin da ya shafi ilimi,tsarin da ƙarin kuɗi  ɓangaren ilimi  ya biyo bayan shi, samar da ayyukan da za su kyautata jin daɗin karatu,ɗaukar Malaman makaranta da horad da su, sai kuma ƙoƙarin da gwamnatin ta ke na samar da hanyar samun ilimi mai inganci.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda rahoton ya nuna,Kano ta samu gaggarumin ci gaba wajen samun babban maki na ayyukan da ake kashe kuɗi don bunƙasa ilimi inda ake amfani da ma’aunin Indeɗ (S-WAESI) abinda ya bata damar samun maki 87.21, inda ta yi ma wasu da yawa waɗanda ake yi masu kallon kamar sun fi kowa dangane da hakan ya satafi sauran wasu gwamnatocin ƙasashe da suka haɗa da, Dakar da kuma Saint-Louis a Senegal. JIhar Legas ce ta ke bi mata, inda ta zama ta 16 a lamarin yadda ake hisabin na sashen yammacin Afirka.

Shi tsarin na S-WAESI yana kallon yadda gwamnatoci sukje mai da hankali kan lamarin ilimi ta hanyar amfani da wasu abubuwan da suka haɗa da yadda aka kashe kuɗin na ɓangaren ilimi,nawa ne ake kashe ma kowane ɗalibi, yadda ake aiwatar da kasafin kuɗin,kashi nawa aka ware ma ilimi, yin abin da gaskiya da kuma sheda kamar yadda aka bada rahoto.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

Ƙarƙashin yadda aka aiwatar, da kashe kuɗin kan lamarin da ya shafi ilimi shi ne ya ke ɗauke da babban maki mai nauyin 35, sai mai bi ma shi, ko nawa  ake kashe ma kowane ɗalibi yana da 25, yadda ake aiwatar da kasafin kuɗin na da 20 yayin da kuma yadda ake ba lamarin ilimi muhimmanci, da sa gaskiya da riƙon amana na asusun kuɗin ko wannensu na da goma-goma.

Rahoton na Jami’ar ta Paris ya bayyana yadda Jihar Kano ta yi har ta kasa da yin  zarra wajen zama jagora wajen mizani kashe kuɗi ƙwarai da gaske babu kama hannun yaro wajen gani da sanin muhimmancin  ilimi shi ne wani ginshiƙin rayuwa, har ta ke kashe maƙudan kuɗaɗe ta hanyar aiwatar da kasafin kuɗin da aka amince a kashe saboda harkar ilimi, shi ya sa ma tafi kowace Jiha ta kashe kuɗi domin raya ilimi, gaba ɗaya a cikin Jihohin ƙasashen ƙawance  na yammacin Afirka  wato ECOWAS a taƙaice.

Shi nazarin ya shafi Jihohi, larduna, ƙaramin lardi, sai kuma wuraren da suke da matakain tamkar ƙaramar hukuma na ƙasashen Nijeriya, Senegal, Ghana, Côte d’Iɓoire, Saliyo, Laberiya, Benin, Burkina Faso, Mali, Nijar, Togo, Guinea, Guinea-Bissau da kuma Cabe Ɓerde.

Kashe kuɗaɗe  masu yawa a tsarin Jihar Kano ya ƙaru ne sannu a hankali a cikin ƴan shekaru ba wasu yawa ba ne. Gwamnatin Jihar ƙarƙashin jagorancin Gwamna Injiniya Abba Kabir Yusuf ya ware ma ɓangaren  na ilimi kashi 29.5 na kasafin kuɗin Jihar na shekara ta 2024, ta haka ne har ya amince abin ya kai kashi 30  na kasafin kuɗin shekarar 2025, inda ya nuna cewa lalle cewar gwamnatin ta nuna ɓangaren ilimi yana daga cikin abubuwan da ta fi ba muhimmanci idan lamarin kashe kuɗaɗen ta ya taso domin raya al’umma.

Kano
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Ba Mu Yarda Da Maƙiyanmu Ba, A Shirye Muke —Iran
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yadda Jihohi Suka Fara Ɗanɗana Ambaliyar Ruwa A Daminar Bana

MASU ALAKA

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
Ilimi

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

July 3, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
Ilimi

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026
Next Post
NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno

NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta'adda A Borno

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno

NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
Gwamna Dauda Ya Raba Buhunan Taki 72,000 Da Kayan Noma Kyauta Ga Manoman Zamfara

Gwamna Dauda Ya Raba Buhunan Taki 72,000 Da Kayan Noma Kyauta Ga Manoman Zamfara

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello

July 11, 2026
Gwamnati Ta Shirya Gina Gidaje 20,000 Duk Shekara Haɗin Gwuiwar  Jamus

Gwamnati Ta Shirya Gina Gidaje 20,000 Duk Shekara Haɗin Gwuiwar Jamus

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ra’ayin Al’umma Game Da Shirin Gwamnati Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 11, 2026
Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

July 11, 2026

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.