Jihar Kano ta kasance jagora da aka ɗauke ta wadda ta ke yin abubuwa ko ayyukan da suka shafi gwamnati a ƙungiyar ƙawancen tattalin arziki kan kashe kuɗin domin lamarin da ya shafi ilimi kamar dai yadda rahoton da Jami’ar Paris ta wallafa na shekarar 2026.
Rahoton ya bayyana Kano ta ɗaya daga cikin gwamnatoci 209 waɗanda suke daga ƙasashe 15 da suke ƴan ƙungiyar ne, inda aka bada misali da Jihar kan yadda take ci gaba da zuba jari sai kuma aiwatar da ayyuka kamar yadda suke a cikin kasafin kuɗi na ilimi.
Yadda Jihar Kanon ta kasance ta ɗaya ya biyo bayan ganin yadda ta bayyana aniyarta ta kafa dokar ta ɓaci kan lamarin da ya shafi ilimi,tsarin da ƙarin kuɗi ɓangaren ilimi ya biyo bayan shi, samar da ayyukan da za su kyautata jin daɗin karatu,ɗaukar Malaman makaranta da horad da su, sai kuma ƙoƙarin da gwamnatin ta ke na samar da hanyar samun ilimi mai inganci.
Kamar yadda rahoton ya nuna,Kano ta samu gaggarumin ci gaba wajen samun babban maki na ayyukan da ake kashe kuɗi don bunƙasa ilimi inda ake amfani da ma’aunin Indeɗ (S-WAESI) abinda ya bata damar samun maki 87.21, inda ta yi ma wasu da yawa waɗanda ake yi masu kallon kamar sun fi kowa dangane da hakan ya satafi sauran wasu gwamnatocin ƙasashe da suka haɗa da, Dakar da kuma Saint-Louis a Senegal. JIhar Legas ce ta ke bi mata, inda ta zama ta 16 a lamarin yadda ake hisabin na sashen yammacin Afirka.
Shi tsarin na S-WAESI yana kallon yadda gwamnatoci sukje mai da hankali kan lamarin ilimi ta hanyar amfani da wasu abubuwan da suka haɗa da yadda aka kashe kuɗin na ɓangaren ilimi,nawa ne ake kashe ma kowane ɗalibi, yadda ake aiwatar da kasafin kuɗin,kashi nawa aka ware ma ilimi, yin abin da gaskiya da kuma sheda kamar yadda aka bada rahoto.
Ƙarƙashin yadda aka aiwatar, da kashe kuɗin kan lamarin da ya shafi ilimi shi ne ya ke ɗauke da babban maki mai nauyin 35, sai mai bi ma shi, ko nawa ake kashe ma kowane ɗalibi yana da 25, yadda ake aiwatar da kasafin kuɗin na da 20 yayin da kuma yadda ake ba lamarin ilimi muhimmanci, da sa gaskiya da riƙon amana na asusun kuɗin ko wannensu na da goma-goma.
Rahoton na Jami’ar ta Paris ya bayyana yadda Jihar Kano ta yi har ta kasa da yin zarra wajen zama jagora wajen mizani kashe kuɗi ƙwarai da gaske babu kama hannun yaro wajen gani da sanin muhimmancin ilimi shi ne wani ginshiƙin rayuwa, har ta ke kashe maƙudan kuɗaɗe ta hanyar aiwatar da kasafin kuɗin da aka amince a kashe saboda harkar ilimi, shi ya sa ma tafi kowace Jiha ta kashe kuɗi domin raya ilimi, gaba ɗaya a cikin Jihohin ƙasashen ƙawance na yammacin Afirka wato ECOWAS a taƙaice.
Shi nazarin ya shafi Jihohi, larduna, ƙaramin lardi, sai kuma wuraren da suke da matakain tamkar ƙaramar hukuma na ƙasashen Nijeriya, Senegal, Ghana, Côte d’Iɓoire, Saliyo, Laberiya, Benin, Burkina Faso, Mali, Nijar, Togo, Guinea, Guinea-Bissau da kuma Cabe Ɓerde.
Kashe kuɗaɗe masu yawa a tsarin Jihar Kano ya ƙaru ne sannu a hankali a cikin ƴan shekaru ba wasu yawa ba ne. Gwamnatin Jihar ƙarƙashin jagorancin Gwamna Injiniya Abba Kabir Yusuf ya ware ma ɓangaren na ilimi kashi 29.5 na kasafin kuɗin Jihar na shekara ta 2024, ta haka ne har ya amince abin ya kai kashi 30 na kasafin kuɗin shekarar 2025, inda ya nuna cewa lalle cewar gwamnatin ta nuna ɓangaren ilimi yana daga cikin abubuwan da ta fi ba muhimmanci idan lamarin kashe kuɗaɗen ta ya taso domin raya al’umma.













