Gwamnatin Jamhuriyar Jama’ar Kasar Sin ita ce halastacciyar gwamnatin da ke wakiltar dukkan kasar Sin, kuma Taiwan wani yanki ne da ba za a iya balle shi daga yankin Sin ba, kamar yadda babban magatakardan Kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai (SCO) Nurlan Yermekbayev ya bayyana a wata hira ta musamman da kamfanin dillancin labarai na Xinhua.
Shugabannin kasashe mambobin kungiyar SCO sun tabbatar da hakan ne a cikin wata sanarwar bayan taron da aka yi mai tarihi a St. Petersburg cikin watan Yunin 2002. Yermekbayev ya bayyana hakan ne a lokacin da aka nemi ya yi tsokaci kan katobarar firaministar Japan Sanae Takaichi game da Taiwan da kuma mummunan alamar da ke nuna cewa Japan na yunkurin farfado da amfani da karfin soja.
Da yake nuni da cewa, a wannan shekarar ce aka cika shekaru 80 da samun nasara a kan mulkin danniya a duniya da kuma kafuwar Majalisar Dinkin Duniya, Yermekbayev ya ce shugabannin kasashe membobin kungiyar SCO sun fitar da sanarwa game da wannan batu a ranar 1 ga watan Satumba a lokacin taron koli na kungiyar ta SCO da ya gudana a Tianjin.
Ya bayar da hujja daga cikin sanarwar cewa, kisan gillar da aka yi wa jama’a yana nuna cewa, amincewa da mulkin kama-karya na Naziyanci (Nazism), da farkisanci (fascism) da amfani da karfin soji, da kuma haifar da kiyayya saboda bambancin launin fata, da kabilanci da addini, da haddasa gaba da nuna wariya, tana haifar da mummunar illa, yayin da kuma nasarar da aka samu a yakin duniya na biyu ta kasance daga sakamakon kokarin da aka yi na hada karfi da karfe a tsakanin dukkan kasashe masu son zaman lafiya.
Kazalika, Yermekbayev ya kara da cewa, sanarwar ta ce kasashen da ke cikin kungiyar suna da alhakin da ya rataya a wuyansu tun daga zamanin baya zuwa na gaba, wato, su ceci zuriya masu zuwa nan gaba daga bala’in yaki da kuma yin bakin kokari wajen hana sake auwar ire-iren wadannan bala’o’i. (Abdulrazaq Yahuza Jere)













