ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babban Taron ‘Yansanda A Zamfara: Dole ’Yan Bindiga Su Miƙa Wuya, Ba Sulhu Tsakanin Mu Da Su— Gwamna Dauda

by Sulaiman
3 weeks ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jaddada cewa ’yan bindigar da suka ƙi zaman lafiya tare da ci gaba da barazana ga rayukan jama’a, musamman a jihar Zamfara dole ne su fuskanci hukunci bisa tanadin doka, babu maganar sulhu da su.

Gwamna Lawal ya bayyana hakan ne a yayin da Gwamnatin Jihar Zamfara ta karɓi baƙuncin wani taron tsaro na musamman kan Arewa maso Yamma, wanda Rundunar ’Yansandan Nijeriya ta shirya, kuma aka fara gudanar da shi ranar Laraba a Fadar Gwamnatin Jihar Zamfara da ke Gusau.

An shirya taron na tsawon kwanaki uku ne da taken “Nazarin Ƙalubalen Tsaro a Yankin Arewa maso Yamma”, tare da halartar Babban Sufeto Janar na ’Yansandan Nijeriya (IGP), Olatunji Rilwan Disu.

ADVERTISEMENT

Mai Magana da Yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris a sanarwar da ya fitar ranar Laraba 19 ga watan Agusta, ya kara da cewa, taron ya haɗa manyan jami’an Rundunar ’Yansandan Nijeriya, wakilan gwamnatocin jihohin Arewa maso Yamma, shugabannin hukumomin tsaro da leƙen asiri, sarakunan gargajiya, shugabannin al’umma da ƙungiyoyin fararen hula.

Da yake buɗe taron, Gwamna Lawal ya yaba wa Sufeto Janar na ’Yansanda da shugabancin Rundunar ’Yansandan Nijeriya bisa shirya taron da kuma zaɓar Zamfara a matsayin jihar da za ta karɓi baƙuncinsa.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

Ya ce, zaɓar Zamfara na da muhimmanci saboda jihar na ɗaya daga cikin wuraren da matsalar tsaro ta fi tsanani a Arewa maso Yamma.A cewarsa, wannan ya sa jihar ta dace da gudanar da cikakken nazari kan matsalolin tsaro da kuma samar da hanyoyin magance su.

Lawal ya ce, matsalar tsaro a yankin ba ta tsaya kan aikata laifuka na yau da kullum ba, domin ƙungiyoyin masu aikata laifuka suna gudanar da garkuwa da mutane da satar shanu a tsakanin iyakokin jihohi.

Ya ce, hakan na barazana ga rayuwar jama’a, samar da abinci, ilimi, zuba jari da zaman lafiyar al’umma.Gwamnan ya kuma yi gargaɗin cewa akwai wasu barazanar tsaro a birane, ciki har da ta’addancin ’yan daba, shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da kutsen masu tsattsauran ra’ayi.

A cewarsa, irin wannan yanayi na buƙatar a daina amfani da martanin tsaro da ya rabu-rabu, domin masu aikata laifuka ba sa kallon iyakokin jihohi. “Dole tsarin tsaronmu ya kasance haɗe wuri guda. Bayanan sirri daga Zamfara na iya hana hari a wata jiha, haka kuma ayyukan tsaro a makwabciyar jiha na iya daƙile barazanar da ke fuskantar Zamfara,” in ji shi.

A nasa jawabin, Sufeto Janar na ’Yansandan Nijeriya, Olatunji Rilwan Disu, ya ce tabbatar da tsaron Arewa maso Yamma alhakin kowa ne, saboda muhimmancin yankin ga Nijeriya.

Ya ce hukumomin tsaro sun haɗa ƙarfi tsakanin jihohi domin tunkarar matsalar rashin tsaro, tare da yin sintiri tare da musayar bayanan sirri.

Disu ya ce rundunar ta yanke shawarar kai farmaki ga masu aikata laifuka maimakon ci gaba da jiran hare-harensu.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

MASU ALAKA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
Manyan Labarai

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Next Post
Ruwa

Gwamnatin Kaduna: Uba Sani Ya Kashe Sama Da N896m Kan Jin Dadin Malaman KASU

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.