Gwamnatin Jihar Kaduna ta bayyana cewa gwamnatin Gwamna Uba Sani ta kashe sama da Naira miliyan 896 wajen kula da jin dadin ma’aikatan Jami’ar Jihar Kaduna (KASU).
Babban Sakataren Gwamna na musamman, Farfesa Bello Ayuba, ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da aka gudanar a Kaduna ranar Laraba, kan wa’adin makonni biyu da kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) reshen KASU ta bai wa gwamnati kafin ta dauki matakin yajin aiki.
Ayuba ya ce ma’aikatan ilimi 59 ne suka bar KASU tun daga watan Janairun 2024 zuwa yanzu, ba 200 ba kamar yadda reshen ASUU-KASU ya yi ikirari.Ya bayyana cewa, ba dukkan ma’aikatan da suka bar jami’ar ne, suka barta sabida rashin kyawun yanayin aiki ba.
Ayuba ya ce, “Yana da kyau ku sani cewa daga watan Janairun 2024 zuwa yanzu, ma’aikatan ilimi 59 ne suka bar jami’ar. Daga cikinsu akwai Farfesoshi da Mataimakan Farfesoshi 17 da suka bar jami’ar bisa radin kansu ko kuma suka sauya wurin aiki.
“Cikin bayanai dalla-dalla, Farfesoshi biyu ne suka bar jami’ar a wannan lokacin, da Mataimakan Farfesoshi biyu, manyan Malamai shida, Malamai masu matsayi na 1 guda 10, matsayi na 2 guda 15, sannan akwai mataimakan malmai guda 12 kowanne su”
Ya kara da cewa sauye-sauyen ma’aikata abu ne da ake samu a jami’o’i saboda yanayin ci gabansu, musamman yadda ake kafa sabbin jami’o’i da kuma samun damar karin matsayi da ke zuwa da su, wanda ke jawo ma’aikata masu mukamai daban-daban.
Ya ce ritayar ma’aikata, da kuma kammala wa’adin ayyukan wucin gadi, ziyara, hutun karatu (sabbatical) da samun kwangiloli, duk suna cikin abubuwan da ke haddasa barin aiki a jami’o’i.
Ayuba ya ce, “Kiran duk irin wadannan sauye-sauyen da ake samu a hukumance da cewa sun faru ne saboda rashin kyawun yanayin aiki, ba tare da gabatar da sahihan bayanai kan dalilan ficewar ma’aikatan ba, babban bata suna ne wanda bai dace da mutanen da ke son ganin an kyautata wurin aikinsu ba.”
Game da jin dadin ma’aikata kuwa, Ayuba ya ce gwamnatin Uba Sani ta ci gaba da nuna jajircewa wajen inganta jin dadin ma’aikatan jami’ar.
Ya ce, “Gwamnatin Uba Sani ba ta yi kasa a gwiwa ba wajen tabbatar da jin dadin ma’aikata. Ya zuwa yanzu, an kashe sama da Naira miliyan 896 wajen jin dadin ma’aikatan jami’ar.”














