Mahukuntan babban yankin kasar Sin sun gabatar da wasu manufofi da matakai guda 10 don kyautata mu’amala ta musaya da kuma hadin gwiwa a tsakanin gabobi 2 na mashigin Taiwan.
Ofishin kula da ayyukan Taiwan na kwamitin tsakiya na jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ya gabatar da jerin abubuwan a yau Lahadi, inda ya ce, yana da burin ci gaba da raya dangantakar da ke tsakanin gabobi 2 na mashigin tekun cikin lumana, da kara dankon zumunci da kyautata jin dadin ‘yan kasa a duk fadin mashigin.
Sanarwar ta zo ne a daidai lokacin da wata tawaga daga jam’iyyar Kuomintang ta kasar Sin, karkashin jagorancin shugabar jam’iyyar Cheng Li-wun, ke kammala ziyarar aiki a babban yankin kasar daga ranar Talata zuwa Lahadin nan.
A cikin wata sanarwa da ofishin ya fitar, ya ce, za a yi kokarin lalubo hanyar tuntubar juna a-kai-a-kai tsakanin jam’iyyar JKS da KMT, kuma za a kafa wani dandali domin inganta mu’amala ta musaya tsakanin matasa na bangarori biyu na mashigin Taiwan.
Kazalika, za a kuma yi kokarin fadada yankunan gabar tekun lardin Fujian, watau babban lardin da ke kusa da Taiwan, don ya samar da ruwan sha, da wutar lantarki, da iskar gas a Kinmen da Matsu, da kuma karfafa aikin gina gadoji da za su ratsa teku don hade yankunan biyu, idan yanayi ya ba da sararin yin hakan.
Har ila yau, kasar Sin za ta hanzarta dawo da zirga-zirgar jiragen sama kai-tsaye a tsakanin gabobi 2 na mashigin Taiwan, ciki har da kai-komon jiragen sama zuwa biranen babban yankin Sin na Urumqi, Xi’an, Harbin, Kunming da kuma Lanzhou. (Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post