Ƙungiyar Arsenal na duba yiwuwar sauya kocinta Mikel Arteta da tsohon ɗan wasanta Cesc Fabregas, wanda yanzu ke jan ragamar ƙungiyar Como a gasar Serie A ta ƙasar Italiya, idan har Arteta ya kasa lashe kofin Firimiya a kakar bana.
Duk da cewa Arsenal na kan gaba a teburin gasar Firimiya, Arteta na fuskantar matsin lamba, musamman ganin yadda Manchester City ke biye da ita a matsayi na biyu kuma na iya kwace gurbin na ɗaya idan ta ci sauran wasanninta.
- Arsenal Ta Samu Ƙwarin Gwiwar Buga Gasar Zakarun Turai Bayan Dawowar ‘Yan Wasanta Biyu
- Arsenal Na Tattaunawa Da Declan Rice Kan Tsawaita Kwantiraginsa A Ƙungiyar
Rahotanni daga kafar yaɗa labarai ta Spain, Mundo Deportivo, sun nuna cewa shugabannin ƙungiyar sun fara tuntuɓar Fabregas domin yiwuwar maye gurbin Arteta a filin wasa na Emirates.
Matsin lambar da Arteta ke fuskanta ya ƙaru ne bayan rashin nasara a hannun Manchester City a wasan ƙarshe na Carabao Cup, da kuma fitar da Arsenal daga kofin FA Cup da Southampton ta yi, tare da rashin nasara a hannun Bournemouth a gasar Firimiya.
Wannan yanayi ya jefa makomar Arteta cikin shakku, yayin da Fabregas ke ci gaba da jan hankalin masu ruwa da tsaki sakamakon irin rawar da yake takawa a Como.













Discussion about this post