Bisa kididdigar da babbar hukumar kwastam ta Sin ta bayar jiya Asabar, a watanni hudu na farkon bana, yawan kudaden kasuwancin shige da fice da Sin ta yi wa kasashen Afirka ya kudin Sin yuan biliyan 885.34, wanda ya karu da kashi 19.4%.
A cewar shugaban sashen kididdiga na babbar hukumar kwastam, Lv Daliang, cikin watanni hudu na farkon bana, yawan kayayyakin da Sin ke shigowa da su daga Afirka ya karu da kashi 11.2% bisa makamancin lokacin bara, wanda ya ci gaba da karuwa cikin watanni 8 a jere. Ban da haka kuma, tun daga ranar 1 ga watan Mayu, Sin ta soke harajin kwastam ga dukkan kasashen Afirka masu huldar diflomasiyya da ita guda 53.
Zuwa yanzu, an riga an ayyana wasu kayayyakin Afirka da dama, ciki har da tuffa, lemun zaki, da avocado, da aka shigo da su Sin a karkashin manufar.
A cewar sabbin bayanai da babbar hukumar kwastam ta fitar, tun daga farkon wannan shekarar, yankunan gabas, da tsakiya da yammacin kasar Sin, da kuma arewa maso gabashin kasar sun yi amfani da fa’idodin da suke da su a fannin yanayin kasa da kuma karfin masana’antu, wanda hakan ya haifar da karuwar ayyukan da ake yi a fannin cinikayyar kasashen waje.
Daga cikinsu, manyan larduna da biranen cinikayyar kasashen waje sun taka muhimmiyar rawa. Misali, a cikin watanni hudu na farko na wannan shekarar, a birnin Yiwu, babbar cibiyar cinikayyar kasashen waje a kasar Sin, yawan shigo da kayayyaki da fitar da su da aka yi, ya kai yuan biliyan 272.23, wanda ya karu da kashi 17.7%.(Safiyah Ma)















Discussion about this post