Ɗan wasan gaba na Nijeriya Victor Osimhen ya yabawa abokan wasansa na Galatasaray bayan ƙungiyar ta lashe kofin gasar Süper Lig ta ƙasar Turkiyya karo na huɗu a jere. Galatasaray ta tabbatar da nasarar lashe kofin ne bayan ta doke Antalyaspor da ci 4-2 a wasan da suka buga ranar Asabar.
Osimhen ya taka muhimmiyar rawa a nasarar ƙungiyar a wannan kakar wasa, inda ya zura ƙwallaye 15 tare da bayar da taimakon cin ƙwallo guda biyar a wasanni 22 da ya buga. Tauraron na Super Eagles ya bayyana farin cikinsa yayin wata hira da kafar yaɗa labarai ta Galatasaray bayan wasan.
Ya ce jajircewa, da haɗin kai da juriyar da ‘yan wasan ƙungiyar suka nuna ne suka taimaka musu wajen samun wannan babban nasara a kakar bana. Osimhen ya kuma yaba da ƙoƙarin magoya bayan ƙungiyar da suka ci gaba da mara musu baya har zuwa ƙarshen kakar.
Da yake an kusa kammala kakar wasa a Turkiyya, Osimhen zai karkata hankalinsa kan wasannin da Nigeria za ta buga a watan gobe ƙarƙashin jagorancin sabon koci Eric Chelle, inda ake sa ran zai ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen taimakawa Super Eagles samun nasara.















Discussion about this post