ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bakar Inuwa, Gwamma Rana Da Ke

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
Bakar inuwa

Su wane ne abokai na jabu? Wato wadanda maimakon su ba ka taimako, sai su nemi haifar maka da karin matsaloli.

Sanin kowa ne, aboki na gaske har kullum yana son ba ka taimako. Misali, a kwanan baya, kasar Sin ta sanar da fara soke dukkan harajin kwastam da ta saka ma kayayyakin kasashe 53 dake nahiyar Afirka, wadanda suka kulla huldar diflomasiyya da ita, ciki har da Najeriya, tun daga ranar 1 ga watan Mayun dake tafe. Wannan manufa za ta taimaki kasashen Afirka wajen fitar da karin kayayyaki zuwa kasar Sin, da raya masana’antu a gidajensu. Ta hanyar rage ribar da ita kanta za ta samu, kasar Sin na neman samar wa abokan hulda karin damammakin raya kasa. Hakan ya nuna niyyar kasar ta zama wata abokiya mai cikakken sahihanci.

Sai dai mene ne abun da kasar Amurka take yi a lokaci daya? A kwanan baya, majalissar wakilai ta kasar Amurka ta fara tantance wani daftarin kundin doka da ya shafi batun ’yancin bin addini a kasar Najeriya. Cikin kundin, an ci gaba da kururuta batun “cin zarafin mutane masu bin addinin Kirista a Najeriya” da na “ayyukan ta’addanci da dakaru ’yan kabilar Fulani suke yi”, kuma an ce wai “Sinawa suna haka ma’adinai ba bisa doka ba a Najeriya, da biyan kudi ga Fulani ’yan bindiga don samun izinin yin haka”. Dangane da zargin da kasar Amurka ta yi, Charles Onunaiju, wani shehun malami mai nazarin harkokin kasar Sin, ya rubuta wani bayanin da aka wallafa shi a jaridar “The Nation” ta Najeriya, inda ya ce kasar Amurka tana shafa wa bangaren Najeriya kashin kaza, tare da neman haddasa husuma tsakanin kasashen Najeriya da Sin.

ADVERTISEMENT

Hakika tuni gwamnatin Najeriya ta kare kanta daga zargin da kasar Amurka ta yi mata, inda ta ce, hare-hare da ayyukan ta’addanci da ake samu a wasu yankunan kasar ba su da alaka da batun addini, kana bai kamata a dora wa wata kabila laifin ta’addanci ba. Kana a nata bangare, kasar Sin ita ma ta yi watsi da zargin da kasar Amurka ta yi, inda ta ce kamfanonin sarrafa ma’adanai na kasar Sin suna kokarin bin dokokin kasar Najeriya, yayin da suke gudanar da ayyukansu a kasar.

Sai dai me ya sa kasar Amurka ke son shafa wa Najeriya da Sin bakin fenti? A cewar Charles Onunaiju, tun daga shekarar 2025, an riga an kaddamar da dimbin masana’antun sarrafa Lithium a kasar Najeriya, wadanda wasu kamfanonin kasar Sin suka zuba musu jari. Batun na alamta cewa, kasar Najeriya za ta sauya daga fitar da danyen sinadari zuwa harkar sarrafa ma’adini don daga darajarsa, ta fuskar aikin raya masana’antun Lithium, da kara taka muhimmiyar rawa a tsarin samar da baturan motoci na duniya. Sai dai a nata bangare, kasar Amurka na kallon Najeriya a matsayin yankin dake karkashin kulawarta, don haka ba ta son ganin yadda kasar Sin ta haifar da karin tasiri kan Najeriya, ko da yake tasiri ne da zai ba Najeriya damammakin raya tattalin arziki da zamantakewar al’umma. Abun da kasar Amurka take yi shi ne, fakewa da zargin da ta yi wa kasashen Najeriya da Sin, don neman rusa alakar dake tsakanin kasashen biyu, duk da cewa hakan zai lalata makomar kasar Najeriya.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Kamar yadda wani mai amfani da shafin sada zumunta na Facebook dan Najeriya mai suna Phils ya fada, “Idan kana tsammanin Amurkawa na kaunar ’yan Najeriya masu bin addinin Krista, to, ni dai na tabbata, wannan ‘kauna’ ta shafi niyyar kare moriyar kasar Amurka ce kawai.”

Batun nan ya tunatar da ni da wani karin magana, wato “Bakar inuwa, gwamma rana da ke.” (Bello Wang)

Bakar inuwa
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya
Bakar inuwa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 5, Sun Ceto Yara 3 A Borno Da Yobe

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.