ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bakar Inuwa, Gwamma Rana Da Ke

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
Bakar inuwa

Su wane ne abokai na jabu? Wato wadanda maimakon su ba ka taimako, sai su nemi haifar maka da karin matsaloli.

Sanin kowa ne, aboki na gaske har kullum yana son ba ka taimako. Misali, a kwanan baya, kasar Sin ta sanar da fara soke dukkan harajin kwastam da ta saka ma kayayyakin kasashe 53 dake nahiyar Afirka, wadanda suka kulla huldar diflomasiyya da ita, ciki har da Najeriya, tun daga ranar 1 ga watan Mayun dake tafe. Wannan manufa za ta taimaki kasashen Afirka wajen fitar da karin kayayyaki zuwa kasar Sin, da raya masana’antu a gidajensu. Ta hanyar rage ribar da ita kanta za ta samu, kasar Sin na neman samar wa abokan hulda karin damammakin raya kasa. Hakan ya nuna niyyar kasar ta zama wata abokiya mai cikakken sahihanci.

Sai dai mene ne abun da kasar Amurka take yi a lokaci daya? A kwanan baya, majalissar wakilai ta kasar Amurka ta fara tantance wani daftarin kundin doka da ya shafi batun ’yancin bin addini a kasar Najeriya. Cikin kundin, an ci gaba da kururuta batun “cin zarafin mutane masu bin addinin Kirista a Najeriya” da na “ayyukan ta’addanci da dakaru ’yan kabilar Fulani suke yi”, kuma an ce wai “Sinawa suna haka ma’adinai ba bisa doka ba a Najeriya, da biyan kudi ga Fulani ’yan bindiga don samun izinin yin haka”. Dangane da zargin da kasar Amurka ta yi, Charles Onunaiju, wani shehun malami mai nazarin harkokin kasar Sin, ya rubuta wani bayanin da aka wallafa shi a jaridar “The Nation” ta Najeriya, inda ya ce kasar Amurka tana shafa wa bangaren Najeriya kashin kaza, tare da neman haddasa husuma tsakanin kasashen Najeriya da Sin.

ADVERTISEMENT

Hakika tuni gwamnatin Najeriya ta kare kanta daga zargin da kasar Amurka ta yi mata, inda ta ce, hare-hare da ayyukan ta’addanci da ake samu a wasu yankunan kasar ba su da alaka da batun addini, kana bai kamata a dora wa wata kabila laifin ta’addanci ba. Kana a nata bangare, kasar Sin ita ma ta yi watsi da zargin da kasar Amurka ta yi, inda ta ce kamfanonin sarrafa ma’adanai na kasar Sin suna kokarin bin dokokin kasar Najeriya, yayin da suke gudanar da ayyukansu a kasar.

Sai dai me ya sa kasar Amurka ke son shafa wa Najeriya da Sin bakin fenti? A cewar Charles Onunaiju, tun daga shekarar 2025, an riga an kaddamar da dimbin masana’antun sarrafa Lithium a kasar Najeriya, wadanda wasu kamfanonin kasar Sin suka zuba musu jari. Batun na alamta cewa, kasar Najeriya za ta sauya daga fitar da danyen sinadari zuwa harkar sarrafa ma’adini don daga darajarsa, ta fuskar aikin raya masana’antun Lithium, da kara taka muhimmiyar rawa a tsarin samar da baturan motoci na duniya. Sai dai a nata bangare, kasar Amurka na kallon Najeriya a matsayin yankin dake karkashin kulawarta, don haka ba ta son ganin yadda kasar Sin ta haifar da karin tasiri kan Najeriya, ko da yake tasiri ne da zai ba Najeriya damammakin raya tattalin arziki da zamantakewar al’umma. Abun da kasar Amurka take yi shi ne, fakewa da zargin da ta yi wa kasashen Najeriya da Sin, don neman rusa alakar dake tsakanin kasashen biyu, duk da cewa hakan zai lalata makomar kasar Najeriya.

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

Kamar yadda wani mai amfani da shafin sada zumunta na Facebook dan Najeriya mai suna Phils ya fada, “Idan kana tsammanin Amurkawa na kaunar ’yan Najeriya masu bin addinin Krista, to, ni dai na tabbata, wannan ‘kauna’ ta shafi niyyar kare moriyar kasar Amurka ce kawai.”

Batun nan ya tunatar da ni da wani karin magana, wato “Bakar inuwa, gwamma rana da ke.” (Bello Wang)

Bakar inuwa
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Bakar inuwa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 5, Sun Ceto Yara 3 A Borno Da Yobe

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.