Su wane ne abokai na jabu? Wato wadanda maimakon su ba ka taimako, sai su nemi haifar maka da karin matsaloli.
Sanin kowa ne, aboki na gaske har kullum yana son ba ka taimako. Misali, a kwanan baya, kasar Sin ta sanar da fara soke dukkan harajin kwastam da ta saka ma kayayyakin kasashe 53 dake nahiyar Afirka, wadanda suka kulla huldar diflomasiyya da ita, ciki har da Najeriya, tun daga ranar 1 ga watan Mayun dake tafe. Wannan manufa za ta taimaki kasashen Afirka wajen fitar da karin kayayyaki zuwa kasar Sin, da raya masana’antu a gidajensu. Ta hanyar rage ribar da ita kanta za ta samu, kasar Sin na neman samar wa abokan hulda karin damammakin raya kasa. Hakan ya nuna niyyar kasar ta zama wata abokiya mai cikakken sahihanci.
Sai dai mene ne abun da kasar Amurka take yi a lokaci daya? A kwanan baya, majalissar wakilai ta kasar Amurka ta fara tantance wani daftarin kundin doka da ya shafi batun ’yancin bin addini a kasar Najeriya. Cikin kundin, an ci gaba da kururuta batun “cin zarafin mutane masu bin addinin Kirista a Najeriya” da na “ayyukan ta’addanci da dakaru ’yan kabilar Fulani suke yi”, kuma an ce wai “Sinawa suna haka ma’adinai ba bisa doka ba a Najeriya, da biyan kudi ga Fulani ’yan bindiga don samun izinin yin haka”. Dangane da zargin da kasar Amurka ta yi, Charles Onunaiju, wani shehun malami mai nazarin harkokin kasar Sin, ya rubuta wani bayanin da aka wallafa shi a jaridar “The Nation” ta Najeriya, inda ya ce kasar Amurka tana shafa wa bangaren Najeriya kashin kaza, tare da neman haddasa husuma tsakanin kasashen Najeriya da Sin.
Hakika tuni gwamnatin Najeriya ta kare kanta daga zargin da kasar Amurka ta yi mata, inda ta ce, hare-hare da ayyukan ta’addanci da ake samu a wasu yankunan kasar ba su da alaka da batun addini, kana bai kamata a dora wa wata kabila laifin ta’addanci ba. Kana a nata bangare, kasar Sin ita ma ta yi watsi da zargin da kasar Amurka ta yi, inda ta ce kamfanonin sarrafa ma’adanai na kasar Sin suna kokarin bin dokokin kasar Najeriya, yayin da suke gudanar da ayyukansu a kasar.
Sai dai me ya sa kasar Amurka ke son shafa wa Najeriya da Sin bakin fenti? A cewar Charles Onunaiju, tun daga shekarar 2025, an riga an kaddamar da dimbin masana’antun sarrafa Lithium a kasar Najeriya, wadanda wasu kamfanonin kasar Sin suka zuba musu jari. Batun na alamta cewa, kasar Najeriya za ta sauya daga fitar da danyen sinadari zuwa harkar sarrafa ma’adini don daga darajarsa, ta fuskar aikin raya masana’antun Lithium, da kara taka muhimmiyar rawa a tsarin samar da baturan motoci na duniya. Sai dai a nata bangare, kasar Amurka na kallon Najeriya a matsayin yankin dake karkashin kulawarta, don haka ba ta son ganin yadda kasar Sin ta haifar da karin tasiri kan Najeriya, ko da yake tasiri ne da zai ba Najeriya damammakin raya tattalin arziki da zamantakewar al’umma. Abun da kasar Amurka take yi shi ne, fakewa da zargin da ta yi wa kasashen Najeriya da Sin, don neman rusa alakar dake tsakanin kasashen biyu, duk da cewa hakan zai lalata makomar kasar Najeriya.
Kamar yadda wani mai amfani da shafin sada zumunta na Facebook dan Najeriya mai suna Phils ya fada, “Idan kana tsammanin Amurkawa na kaunar ’yan Najeriya masu bin addinin Krista, to, ni dai na tabbata, wannan ‘kauna’ ta shafi niyyar kare moriyar kasar Amurka ce kawai.”
Batun nan ya tunatar da ni da wani karin magana, wato “Bakar inuwa, gwamma rana da ke.” (Bello Wang)















Discussion about this post