ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ban Janye Wa Kowa Takarata Ba – Sani Sha’aban

by Idris Umar
4 years ago
Takarata

Dan takarar kujerar gwamna a jihar Kaduna a karkashin jam’iyyar ADP, Honorabul Sani Sha’aban, ya bayyana cewa maganganun da wasu ke yi cewa ya janye takararsa bai san wannan zancen ba, domin kuwa shi ma ji ya yi kamar al’mara.

Dan takarar, wanda ya bayyana cewa duka ‘yan takarar da ke neman gwamna a jihar Kaduna ‘yan uwa ne domin duk daga Zazzau suka fito, ya bayyana cewa shi bai kullaci kowa ba kuma ba ya da niyyar kullatar wani a zuciyarsa.

  • Jami’in Najeriya: Inganta Samun Wadata Tare Zai Samar Da Karin Kuzari Ga Ci Gaban Kasar Sin
  • Zaben Gwamnoni: Jihohin Da Za A Fafata Mai Tsanani

Dan takarar, wanda ke magana a cikin wata hira da aka yi da shi ta musamman, ya bayyana maganganun janyewar ta sa har sun bata ran cibiyar jam’iyyar ta kasa, inda ya ce, “Abin har ya batawa cibiyar jam’iyyar rai har sun saki sanarwa a kan cewa ADP mai littafi babu inda ta je ta zauna ta ce dantakarar ta ya sauka.”

ADVERTISEMENT

Ya ma bayyana cewa suna ziyartar juna, ana zumunci tunda ‘yan siyasa suke, amma dai ba a yi yarjejeniya da shi ba.

Dangane da nasararsa, ya bayyana cewa tafiyarsa ta riga ta yi nisa, babu abinda zai cewa Allah sai godiya, inda ya bayyana cewa jam’iyyar LP ta yi karfi a Kaduna, amma kashi 80 sun koma ADP.

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

Da ya ke magana dangane da salon yakin neman zabensa, sai ya bayyana cewa tafiyar 2007 daban ta ke da ta 2011, ita kuma daban ta ke da shekarar 2015, domin a misalin da ya bayar, takarar Buhari akwai lokacin da ake da Boko Haram, akwai lokacin da in za ka tafi Abuja daga Zazzau za ka dunga ganin shingayen sojoji, sai ya ce a kamfe din sa ba ya kwasar motoci masu yawa ya tafi, mutane ke bi wuri zuwa wuri da hotonsa su roki alfarma, ya kan kuma tara mutane na unguwa a sha shayi tare ya gansu su ganshi, ba a ganin tawagarsa domin kada ya sa mutane cikin hadari.

Dan takarar ya bayyana cewa mutane na matukar son takararsa, ana tsayar da shi a gefen titi, a wurin taro, wurin jana’iza a nuna ana so ya fito, wasu ma sun bar jam’iyyun su sun dawo tafiyarsa, inda ya ce kashi 75 na mutanen Kaduna sun yi amanna sun karanta zuciyarsa sun yarda lallai akwai wani nono da zai tarfa a garinsu.

Dan takarar wanda ya yi bayani dangane da irin wahalar da mutane ke fuskanta a bangaren karin kudin makaranta da ilimi, ya bayyana cewa fastocinsa wasu ke yi, huluna da kananan riguna, da tallarsa al’umma ke yi kuma musulmai da kiristoci.

Takarata
Idris Umar
+ postsBio
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    Sanata Shehu Sani Ya Nemi Gwamnonin Arewa Su Tallafa Wa Bikin Al’adu Na ABU Zariya
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    Yadda Dakta A’isha Mustapha Ta Zama Shugabar Ƙungiyar Likitocin Jihar Kaduna
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    Kafafen Sadarwa Na Zamani Wuri Ne Na Bunƙasa Tattalin Arziƙi — Ubale Kiru
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    Kungiyar Daliban Jami’ar ABU Ta Gudanar Gasar Girke-girken Abincin Gargajiya A Bude Bikin Al’adu Na Bana

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Next Post
Jami’in Afirka ta kudu: Tsarin Demokuradiyya Na Sin Ya Mayar Da Hankali Kan Jama’ar Kasar

Jami’in Afirka ta kudu: Tsarin Demokuradiyya Na Sin Ya Mayar Da Hankali Kan Jama’ar Kasar

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.