ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ban Janye Wa Kowa Takarata Ba – Sani Sha’aban

by Idris Umar
3 years ago
Takarata

Dan takarar kujerar gwamna a jihar Kaduna a karkashin jam’iyyar ADP, Honorabul Sani Sha’aban, ya bayyana cewa maganganun da wasu ke yi cewa ya janye takararsa bai san wannan zancen ba, domin kuwa shi ma ji ya yi kamar al’mara.

Dan takarar, wanda ya bayyana cewa duka ‘yan takarar da ke neman gwamna a jihar Kaduna ‘yan uwa ne domin duk daga Zazzau suka fito, ya bayyana cewa shi bai kullaci kowa ba kuma ba ya da niyyar kullatar wani a zuciyarsa.

  • Jami’in Najeriya: Inganta Samun Wadata Tare Zai Samar Da Karin Kuzari Ga Ci Gaban Kasar Sin
  • Zaben Gwamnoni: Jihohin Da Za A Fafata Mai Tsanani

Dan takarar, wanda ke magana a cikin wata hira da aka yi da shi ta musamman, ya bayyana maganganun janyewar ta sa har sun bata ran cibiyar jam’iyyar ta kasa, inda ya ce, “Abin har ya batawa cibiyar jam’iyyar rai har sun saki sanarwa a kan cewa ADP mai littafi babu inda ta je ta zauna ta ce dantakarar ta ya sauka.”

ADVERTISEMENT

Ya ma bayyana cewa suna ziyartar juna, ana zumunci tunda ‘yan siyasa suke, amma dai ba a yi yarjejeniya da shi ba.

Dangane da nasararsa, ya bayyana cewa tafiyarsa ta riga ta yi nisa, babu abinda zai cewa Allah sai godiya, inda ya bayyana cewa jam’iyyar LP ta yi karfi a Kaduna, amma kashi 80 sun koma ADP.

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Da ya ke magana dangane da salon yakin neman zabensa, sai ya bayyana cewa tafiyar 2007 daban ta ke da ta 2011, ita kuma daban ta ke da shekarar 2015, domin a misalin da ya bayar, takarar Buhari akwai lokacin da ake da Boko Haram, akwai lokacin da in za ka tafi Abuja daga Zazzau za ka dunga ganin shingayen sojoji, sai ya ce a kamfe din sa ba ya kwasar motoci masu yawa ya tafi, mutane ke bi wuri zuwa wuri da hotonsa su roki alfarma, ya kan kuma tara mutane na unguwa a sha shayi tare ya gansu su ganshi, ba a ganin tawagarsa domin kada ya sa mutane cikin hadari.

Dan takarar ya bayyana cewa mutane na matukar son takararsa, ana tsayar da shi a gefen titi, a wurin taro, wurin jana’iza a nuna ana so ya fito, wasu ma sun bar jam’iyyun su sun dawo tafiyarsa, inda ya ce kashi 75 na mutanen Kaduna sun yi amanna sun karanta zuciyarsa sun yarda lallai akwai wani nono da zai tarfa a garinsu.

Dan takarar wanda ya yi bayani dangane da irin wahalar da mutane ke fuskanta a bangaren karin kudin makaranta da ilimi, ya bayyana cewa fastocinsa wasu ke yi, huluna da kananan riguna, da tallarsa al’umma ke yi kuma musulmai da kiristoci.

Takarata
Idris Umar
+ postsBio
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

MASU ALAKA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
Labarai

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
Labarai

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Next Post
Jami’in Afirka ta kudu: Tsarin Demokuradiyya Na Sin Ya Mayar Da Hankali Kan Jama’ar Kasar

Jami’in Afirka ta kudu: Tsarin Demokuradiyya Na Sin Ya Mayar Da Hankali Kan Jama’ar Kasar

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.