ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Shekara 9, Gwamnan Zamfara Ya Warware Matsalar Ɗaliban Jami’ar Crescent

by Sulaiman
8 months ago
Zamfara

Gwamna Lawal Ya Bai Wa Ɗalibai 50 Na Jami’ar Crescent Takardun Kammala Karatu

 

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya miƙa wa ɗalibai 50 takardun shaidar kammala karatu daga Jami’ar Crescent da ke Abeokuta, waɗanda gwamnatin jihar ta ɗauki nauyin karatunsu a baya.

 

ADVERTISEMENT

An gudanar da taron miƙa takardun ne a ranar Alhamis a Babban Zauren Gidan Gwamnati da ke Gusau.

  • Majalisar Dokokin Legas Ta Amince Da Kasafin Tiriliyan ₦4.4 Na Shekarar 2026
  • Yawan Fasinjojin Da Jiragen Kasa Suka Yi Jigilarsu a Kasar Sin Ya Zarce Biliyan 4.5 A Shekarar 2025

Mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya bayyana cewa waɗannan ɗalibai sun kammala karatunsu tun shekaru tara da suka wuce, amma suka kasance cikin mawuyacin hali sakamakon rashin biyan kuɗaɗen makaranta daga gwamnatocin da suka gabata.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

 

A cewarsa, Jami’ar Crescent ta ƙi sakin sakamakon ɗaliban ne saboda rashin biyan kuɗaɗen karatun da aka tara tsawon shekaru, lamarin da ya jefa su cikin rashin tabbas da damuwa.

 

Sanarwar ta ce, bayan gwamnatin Gwamna Lawal ta yi nazari mai zurfi kan lamarin, ta tuntubi jami’ar tare da biyan dukkan basussukan kuɗaɗen karatun da ake bi. Wannan mataki ne da ya bai wa ɗaliban damar karbar sakamakonsu da kuma takardun kammala karatu bayan dogon lokaci suna jira.

 

Daga cikin ɗaliban 50 da suka amfana, akwai wanda ya samu matakin First Class a fannin Kimiyya (Chemistry), tare da wasu da dama da suka kammala karatu da sakamako mai daraja na Second Class Upper, abin da ya ƙara haskaka ƙwarewa da jajircewar ɗaliban duk da ƙalubalen da suka fuskanta.

 

Yayin miƙa takardun, Gwamna Lawal ya jaddada cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da ba da fifiko ga ilimi a matsayin ginshiƙin ci gaba. Ya ce wannan mataki ya yi daidai da manufar gwamnatinsa ta ayyana dokar ta-baci a bangaren ilimi, wadda tuni ta fara haifar da sakamako mai kyau.

 

Gwamnan ya kuma yi kira ga ɗaliban da su yi amfani da damar da suka samu wajen zama jakadu nagari ga jihar Zamfara, tare da bayar da gudunmawa wajen gina ƙasa da al’umma.

 

A cewar sanarwar, wannan aiki na gwamnan ya ƙara nuna aniyar gwamnatinsa ta gyara kura-kuran da suka faru a baya tare da tabbatar da cewa ɗaliban jihar ba za su sake shiga irin wannan mawuyacin hali ba a gaba.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace
  • Sulaiman
    Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana
Labarai

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Next Post
Hadarin Kwale-Kwale

Hadurran Kwale-kwale: Al’ummomin Yankunan Na Neman Daukin Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.