ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadurran Kwale-kwale: Al’ummomin Yankunan Na Neman Daukin Gwamnati

by Sani Anwar and Sulaiman
6 months ago
Hadarin Kwale-Kwale

Al’ummar Jihohin Sakkwato da Neja da Kogi da Yobe, sun nemi daukin gwamnatin tarayya, kan yawaitar haduran kwale-kwale, musamman ganin irin yadda yake cin rayukan al’umma lokaci bayan lokaci.

Ana danganta yawancin haduran ne da amfani da kwale-kwale marasa inganci da kuma daukar mutane fiye da kima, a kan haka ne ake ganin hukumomin kula da tafiye-tafiye a ruwa da kuma hukumomin bayar da agaji, su sanya ido tare da hukunta wadanda aka samu da sakaci a afkuwar haduran kwale-kwalen.

  • Sin Ta Ce Ficewar Amurka Daga Hukumomin Kasa Da Kasa 66 Ba Sabon Abu Ba Ne
  • Majalisar Dokokin Legas Ta Amince Da Kasafin Tiriliyan ₦4.4 Na Shekarar 2026

A wani mataki na yunkurin kawo karshen yawaitar mace-mace a magudanan ruwa na Nijeriya, mazauna Karamar Hukumar Nguru da ke Jihar Yobe, sun yi kira ga gwamnatin tarayya; da ta dauki matakin gaggawa na kare ci gaba da afkuwar haduran jiragen ruwa.

ADVERTISEMENT

Wasu daga cikin mazauna yankin, sun zanta da LEADERSHIP, bayan hadarin da ya afku a yankin, inda suka ce; kimanin mutum 29 ne suka rasa rayukansu a daren ranar Asabar.

Daya daga cikin mazauna yankin, Malam Abubakar Ali, ya bukaci gwamnati da ta tabbatar da cewa; kwale-kwalen da ake amfani da su, suna dauke da injina masu kyau tare kuma da samar da rigunan ceto.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Ya kara da cewa, tilas ne a tilasta wa masu gudanar da aikin, mutunta iyakokin kwale-kwalen da kaucewa yin lodin kaya da kuma yin tafiye-tafiye da daddare.

Daya daga cikin Hakimai, wanda ya nemi a sakaya sunansa ya bayyana cewa; kwale-kwalen, na daukar fasinjoji fiye da kima, wanda hakan ke sanadiyar haifar da hadarurruka daban-daban.

Wani dan kasuwa a garin, mai suna Alhaji Musa Bello, ya bayyna cewa; ya ji takaicin lamarin da ya kusan hallaka iyalansa baki-daya, yana mai bayyana lamarin a matsayin mai matukar radadi tare da ban tausayi.

“Na yi matukar bakin ciki sosai, game da hatsarin jirgin ruwan da ya afku, don haka; akwai bukatar samar da matakai, domin kauce wa sake faruwar wannan hadari a nan gaba,” in ji shi.

A wani labarin kuma, Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya kai ziyarar jajanta wa Masarautar Nguru, musamman al’ummar Garbi, a ranar Litinin 5 ga watan Janairun 2026, biyo bayan wani mummunan hatsarin jirgin ruwa da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama.

Gwamnan, wanda ya jagoranci wata babbar tawaga zuwa Nguru, ya samu wakilcin mataimakinsa, Hon. Idi Barde Gubana.

Buni ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici da kuma matukar radadi, inda ya bukaci al’ummar yankin Garbi da Kauyen Adiyani da ke Jihar Jigawa, da su dauki afkuwar a’lamarin a matsayin wani iftila’i daga Allah SWT.

Da yake jajanta wa iyalan wadanda suka mutu, gwamnan ya bayyana cewa; a musulunci, duk wadanda suka mutu ta hanyar nutsewa a ruwa, ana daukarsu a matsayin shahidai (Shaheed), wadanda suke samun rahama ta musamman daga wajen ubangiji, idan aka yi la’akari da irin radadin mutuwar tasu.

Har ila yau, ya yi addu’ar Allah ya ji kan wadanda suka mutun, ya kuma sa Aljanna ce makomarsu.

Gwamnan, ya kuma sanar da bayar da tallafin kudi da ya kai kimanin naira miliyan 20 tare da bayar da naira 500,000 ga iyalan kowannen wadanda suka rasa rayukan nasu, sannan kuma; an bai wa wadanda suka samu raunuka kyautar naira 200,000 kowannensu.

Ya kara da cewa, a yunkurin sake hana afkuwar lamarin a nan gaba, Gwamna Buni, ya umarci Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar (SEMA), da ta shirya horo na musamman tare da wayar da kan masu sana’ar ta kwale-kwale a cikin gida, domin kiyaye hadarin da ke tattare da ruwa.

Ya kuma bayyana shirin da gwamnatin jihar ta yi na sayo rigunan ceto da sauran kayayyakin kariya, da kwale-kwalen lantarki na zamani, yayin da ya gargadi masu amfani da su kan yin mummunan lodin kwale-kwale da fasinjoji da sauran kayayyaki.

Shi ma da yake yin nasa jawabin, dan majalisa mai wakiltar Nguru, Machina, Yusufari da Karasuwa, Hon. Tijjani Zannah Zakariyya, tare da Sakataren Gwamnatin Jihar Yobe, Alhaji Baba Mallam Wali, ya bukaci al’ummar da abin ya shafa, da su ci gaba da yi wa wadanda suka rasu addu’ar Allah ya gafarta musu da kuma neman lafiya ko ceto wadanda har yanzu ba a gan su ba.

Sakataren zartarwa na Hukumar SEMA, Dakta Mohammed Goje, ya bayyana cewa; lamarin ya faru ne a ranar Asabar 3 ga watan Janairun 2026, inda wani kwale-kwalen da ke dauke da fasinjoji kusan 52, wadanda yawancinsu masunta ne da ‘yan kasuwa daga Kauyen Adiyani da ke Jihar Jigawa zuwa Garbi a Karamar Hukumar Nguru ya kife.

Ya bayyana cewa, an tabbatar da mutuwar mutum 29 tare da ceto mutum 15 da ransu, yayin da takwas kuma suka bace, har zuwa tattara wannan rahoto, babu duriyarsu.

Goje ya kara da cewa, ana ci gaba da aikin bincike domin ceto su, wanda masu ruwa da tsaki na cikin gida da masu kwale-kwale ke gudanarwa, karkashin kulawar hukumar ta SEMA.

Ya ci gaba da cewa, hukumar ta kammala tantance kayan abinci ga daukacin fasinjoji 52, sannan kuma za ta ci gaba da neman wadanda har yanzu ba a san inda suke ba.

Gwamna Mai Mala Buni, ya yi ta’aziyya tare da bayar da gudunmawar naira miliyan 20 da kuma bayar da umarnin yin gyare-gyare ta fuskar harkokin kula da tsaro da rigunan ruwa da kwale-kwale na zamani da kuma horar da matuka jiragen.

Wani bincike da aka aiwatar ya binciko cewa, yawancin abubuwan da suka faru a jihohi kamar Sakkwato, Neja, Kogi da Yobe, na nuni ne da cewa, abubuwa ne da za a iya magance su.

Kwale
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Kwale
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
  • Sulaiman
    Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Next Post
Shugaba Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Kaddamar Da Shekarar Cudanyar Al’ummun Sin Da Afirka

Shugaba Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Kaddamar Da Shekarar Cudanyar Al’ummun Sin Da Afirka

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.