A yau Litinin ne aka gudanar da taron karawa juna sani, game da gina jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin a birnin Beijing. Taron ya bayyana yadda tun bayan babban taron wakilan jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin na 18, wanda ya gudana a shekarar 2012, kwamitin kolin JKS da ya mayar da Xi Jinping a matsayin jigo, ya ci gaba da gabatar da sabbin jerin dabaru, da tunani, da tsare-tsare na shawo kan manyan batutuwan lokutan da aka shiga.
Kazalika, sun himmatu wajen tsara nau’in salon Markisanci na jam’iyya da ake bukata don gudanar da gwamnati ta dogon lokaci, da ma yadda za a cimma nasarar kafa jam’iyyar. A kan wannan turba ne kuma, aka samar da tunanin Xi Jinping dangane da gina jam’iyya, kamar dai yadda taron ya bayyana.
Taron ya kuma ce wannan tunani da ya zamo muhimmin bangare cikin tunanin Xi Jinping, dangane da salon gurguzu mai halayyar musamman na kasar Sin a sabon zamani, ya samar da jerin gudummawar ainihi ga bunkasar akidar Markisanci ta gina jam’iyya, da babban muhimmanci ta fuskar aiwatarwa, da jagoranci mai fadi don karfafa jam’iyya da kasa. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post