Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya ce kasarsa ta yi maraba da yarjejeniyar fahimtar juna da aka cimma tsakanin Amurka da Iran, ta kuma jinjinawa kwazon Pakistan na shiga tsakani.
Lin Jian, ya bayyana hakan ne a Litinin din nan, yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa, yana mai cewa Sin na fatan Amurka da Iran za su sanya hannu kan kason farko na yarjejeniyar a kan lokaci, kuma dukkanin sassa masu ruwa da tsaki za su nacewa matakan shawo kan rikicin ta hanyar lumana, da warware dukkanin batutuwa ta tattaunawa da gudanar da shawarwari.
Daga nan sai jami’in ya bayyana aniyar kasar Sin, ta yin aiki tare da sassan kasa da kasa wajen ci gaba da taka rawar da ta dace, don gaggauta dawo da zaman lafiya da lumana a Gabas ta Tsakiya.
Lin Jian, ya ce Sin na fatan za a kai ga gaggauta sake bude mashigin Hormuz, ta yadda zirga-zirga za ta dawo lami lafiya ba tare da wani kaidi ba. Kazalika, Sin a shirye take ta wanzar da tuntuba tare da kasashen shiyyar, da ma sauran sassan kasa da kasa kan batutuwa masu nasaba da hakan. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post