ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Aminu Bayero Ya Samu Nakasu Ta Ɓangaren Siyasa

by Sulaiman and Bello Hamza
39 minutes ago
Bayero

Muhammad Sanusi da Aminu Ado Bayero, wadanda ke jayayya kan wane ne hakikanin Sarkin Kano, a watan da ya gabata an tilasta musu su dakatar da shirye-shiryensu na gudanar da hawan Sallah a jihar.

Canjin da aka tilasta musu ya biyo bayan umarnin rudunar ‘yansanda ta Jihar Kano, saboda tsoron yiwuwar samun tashin hankali. Amma watakila wannan ne karo na karshe da sarakunan biyu za su yi yunkurin gudanar da bukukuwan al’ada masu hamayya.Daga dukkan alamu, rikicin kan masarautar ba za a iya warware shi ba ta hanyar siyasa ba tare da samun yarda ko tattaunawa da Sanusi ko Bayero ba. Sun fara rikicin ne tun a watan Yuni 2024.A cewar dokar jihar, gwamnan jihar ne ke da ikon nada sarkin kuma majalisar jihar ke tabbatar da nadin. An cire Sanusi a 2020, aka maye gurbinsa da Bayero, sannan ya koma a 2024.Haka kuma an samu rudani a tsakanin iyalan gidan Bayero. Ganduje ya yi alkawarin sanya ’yan’uwa guda biyu Sarkin Kano a shekarar 2020. Daga karshe ya raba sarautar zuwa gida biyar, inda ya nada Sarkin Bichi.

Takaddama tsakanin Bayero da Sanusi kan wanda ya dace ya zama Sarkin Kano, ya zama rikici a tsakanin iyali guda biyu, ya kasance tasirin siyasa ne a tsakanin Abdullahi Ganduje da Rabiu Kwankwaso, da kuma gwagwarmayar doka wadda ke gwada iyakokin kotunan tarayya wajen shiga cikin lamarin ikon kotunan jihar.An shigar da kararraki da dama a gaban babbar kotun Jihar Kano da kuma manyan kotunan tayayya. An dai dakatar da dukkan shari’o’in tun daga 2024.

ADVERTISEMENT

Lamarin ya kuma kai wurin Shugaban kasa, Bola Tinubu, wanda ya ga sauke Bayero a matsayin cin fuska ga shugabancinsa. A shekarar 2014, an yi amfani da masarautar wajen gudanar da mabanbantan ra’ayoyi don kalubalantar shugabancin Goodluck Jonathan.

A karshen shekarar 2025, an yi fatan cewa rikicin zai kawo karshe bayan Gwamna Abba Yusuf ya sauya sheka daga jam’iyyar Kwankwaso zuwa na Tinubu, wanda ya sanya shi cikin rukuni daya da Ganduje.Bayan shiga jam’iyyar gwamnati, Yusuf ya bayyana cewa ba shi da shirin cire Sanusi. Yayin da Sanusi da Yusuf sun auri ’yan’uwan Bayero.

LABARAI MASU NASABA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

Rahotannin sun nuna cewa wasu bangarorin siyasa a cikin APC mai mulki a Kano, ciki har da bangaren Yusuf da Ganduje, sun yi watsi da duk wani yukuri ya kiran Bayero a matsayin Sarkin Kano.

Domin hada kowane bangare cikin APC, an ce bangaren Ganduje ya kafa wasu sharudda ga Yusuf. Wani bangare na sharadin shi ne, zabi tsakanin mataimakin gwamna domin maye gurbin Aminu Abdulsalam wanda ya yi murabus, saboda biyayya ga Kwankwaso, ko kuma zabi wanda zai zama Sarkin Kano.A ranar 27 ga Afrilu, an tabbatar da Murtala Sule Garo, mai biyayya ga Ganduje, a matsayin mataimakin gwamna ga majalisar jihar, sannan daga baya aka rantsar da shi ya shiga ofis.Babu wasu rahotanni da ke cewa Tinubu ya tuntubi Bayero ko ya nuna goyon baya a tsakanin bangarorin APC a Kano. Dukkan Sanusi da Bayero makomansu na ga hannun ‘yan siyasa. Dole daya daga cikinsu ne za a amince da shi a matsayin Sarkin Kano

Bayero
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Beijing: An Gudanar Da Taron Karawa Juna Sani Game Da Gina JKS
  • Sulaiman
    Ruben Amorim Na Dab Da Zama Sabon Kocin AC Milan
  • Sulaiman
    Gwamnati Ta Ɗora Alhakin Tashin Farashin Gas Kan Canjin Kuɗaɗen Waje da Sauransu
  • Sulaiman
    Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a
Bayero
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

MASU ALAKA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
Ra'ayinmu

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

May 29, 2026
Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
Labarai

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

May 22, 2026
Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Ra'ayinmu

Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

May 15, 2026

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Aminu Bayero Ya Samu Nakasu Ta Ɓangaren Siyasa

Aminu Bayero Ya Samu Nakasu Ta Ɓangaren Siyasa

June 15, 2026
Beijing: An Gudanar Da Taron Karawa Juna Sani Game Da Gina JKS

Beijing: An Gudanar Da Taron Karawa Juna Sani Game Da Gina JKS

June 15, 2026
Ruben Amorim Na Dab Da Zama Sabon Kocin AC Milan

Ruben Amorim Na Dab Da Zama Sabon Kocin AC Milan

June 15, 2026
Gwamnati Ta Ɗora Alhakin Tashin Farashin Gas Kan Canjin Kuɗaɗen Waje da Sauransu

Gwamnati Ta Ɗora Alhakin Tashin Farashin Gas Kan Canjin Kuɗaɗen Waje da Sauransu

June 15, 2026
Tunisiyya Ta Sallami Kocinta Bayan Shan Kashi 5-1 A Wasan Farko Na Kofin Duniya

Tunisiyya Ta Sallami Kocinta Bayan Shan Kashi 5-1 A Wasan Farko Na Kofin Duniya

June 15, 2026
Kotu Ta Umarci INEC Ta Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu 4

Kotu Ta Umarci INEC Ta Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu 4

June 15, 2026
ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

June 15, 2026
Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

June 15, 2026
Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

June 15, 2026
Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

June 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.