Muhammad Sanusi da Aminu Ado Bayero, wadanda ke jayayya kan wane ne hakikanin Sarkin Kano, a watan da ya gabata an tilasta musu su dakatar da shirye-shiryensu na gudanar da hawan Sallah a jihar.
Canjin da aka tilasta musu ya biyo bayan umarnin rudunar ‘yansanda ta Jihar Kano, saboda tsoron yiwuwar samun tashin hankali. Amma watakila wannan ne karo na karshe da sarakunan biyu za su yi yunkurin gudanar da bukukuwan al’ada masu hamayya.Daga dukkan alamu, rikicin kan masarautar ba za a iya warware shi ba ta hanyar siyasa ba tare da samun yarda ko tattaunawa da Sanusi ko Bayero ba. Sun fara rikicin ne tun a watan Yuni 2024.A cewar dokar jihar, gwamnan jihar ne ke da ikon nada sarkin kuma majalisar jihar ke tabbatar da nadin. An cire Sanusi a 2020, aka maye gurbinsa da Bayero, sannan ya koma a 2024.Haka kuma an samu rudani a tsakanin iyalan gidan Bayero. Ganduje ya yi alkawarin sanya ’yan’uwa guda biyu Sarkin Kano a shekarar 2020. Daga karshe ya raba sarautar zuwa gida biyar, inda ya nada Sarkin Bichi.
Takaddama tsakanin Bayero da Sanusi kan wanda ya dace ya zama Sarkin Kano, ya zama rikici a tsakanin iyali guda biyu, ya kasance tasirin siyasa ne a tsakanin Abdullahi Ganduje da Rabiu Kwankwaso, da kuma gwagwarmayar doka wadda ke gwada iyakokin kotunan tarayya wajen shiga cikin lamarin ikon kotunan jihar.An shigar da kararraki da dama a gaban babbar kotun Jihar Kano da kuma manyan kotunan tayayya. An dai dakatar da dukkan shari’o’in tun daga 2024.
Lamarin ya kuma kai wurin Shugaban kasa, Bola Tinubu, wanda ya ga sauke Bayero a matsayin cin fuska ga shugabancinsa. A shekarar 2014, an yi amfani da masarautar wajen gudanar da mabanbantan ra’ayoyi don kalubalantar shugabancin Goodluck Jonathan.
A karshen shekarar 2025, an yi fatan cewa rikicin zai kawo karshe bayan Gwamna Abba Yusuf ya sauya sheka daga jam’iyyar Kwankwaso zuwa na Tinubu, wanda ya sanya shi cikin rukuni daya da Ganduje.Bayan shiga jam’iyyar gwamnati, Yusuf ya bayyana cewa ba shi da shirin cire Sanusi. Yayin da Sanusi da Yusuf sun auri ’yan’uwan Bayero.
Rahotannin sun nuna cewa wasu bangarorin siyasa a cikin APC mai mulki a Kano, ciki har da bangaren Yusuf da Ganduje, sun yi watsi da duk wani yukuri ya kiran Bayero a matsayin Sarkin Kano.
Domin hada kowane bangare cikin APC, an ce bangaren Ganduje ya kafa wasu sharudda ga Yusuf. Wani bangare na sharadin shi ne, zabi tsakanin mataimakin gwamna domin maye gurbin Aminu Abdulsalam wanda ya yi murabus, saboda biyayya ga Kwankwaso, ko kuma zabi wanda zai zama Sarkin Kano.A ranar 27 ga Afrilu, an tabbatar da Murtala Sule Garo, mai biyayya ga Ganduje, a matsayin mataimakin gwamna ga majalisar jihar, sannan daga baya aka rantsar da shi ya shiga ofis.Babu wasu rahotanni da ke cewa Tinubu ya tuntubi Bayero ko ya nuna goyon baya a tsakanin bangarorin APC a Kano. Dukkan Sanusi da Bayero makomansu na ga hannun ‘yan siyasa. Dole daya daga cikinsu ne za a amince da shi a matsayin Sarkin Kano














Discussion about this post