ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Aminu Bayero Ya Samu Nakasu Ta Ɓangaren Siyasa

by Sulaiman and Bello Hamza
1 month ago
Bayero

Muhammad Sanusi da Aminu Ado Bayero, wadanda ke jayayya kan wane ne hakikanin Sarkin Kano, a watan da ya gabata an tilasta musu su dakatar da shirye-shiryensu na gudanar da hawan Sallah a jihar.

Canjin da aka tilasta musu ya biyo bayan umarnin rudunar ‘yansanda ta Jihar Kano, saboda tsoron yiwuwar samun tashin hankali. Amma watakila wannan ne karo na karshe da sarakunan biyu za su yi yunkurin gudanar da bukukuwan al’ada masu hamayya.Daga dukkan alamu, rikicin kan masarautar ba za a iya warware shi ba ta hanyar siyasa ba tare da samun yarda ko tattaunawa da Sanusi ko Bayero ba. Sun fara rikicin ne tun a watan Yuni 2024.A cewar dokar jihar, gwamnan jihar ne ke da ikon nada sarkin kuma majalisar jihar ke tabbatar da nadin. An cire Sanusi a 2020, aka maye gurbinsa da Bayero, sannan ya koma a 2024.Haka kuma an samu rudani a tsakanin iyalan gidan Bayero. Ganduje ya yi alkawarin sanya ’yan’uwa guda biyu Sarkin Kano a shekarar 2020. Daga karshe ya raba sarautar zuwa gida biyar, inda ya nada Sarkin Bichi.

Takaddama tsakanin Bayero da Sanusi kan wanda ya dace ya zama Sarkin Kano, ya zama rikici a tsakanin iyali guda biyu, ya kasance tasirin siyasa ne a tsakanin Abdullahi Ganduje da Rabiu Kwankwaso, da kuma gwagwarmayar doka wadda ke gwada iyakokin kotunan tarayya wajen shiga cikin lamarin ikon kotunan jihar.An shigar da kararraki da dama a gaban babbar kotun Jihar Kano da kuma manyan kotunan tayayya. An dai dakatar da dukkan shari’o’in tun daga 2024.

ADVERTISEMENT

Lamarin ya kuma kai wurin Shugaban kasa, Bola Tinubu, wanda ya ga sauke Bayero a matsayin cin fuska ga shugabancinsa. A shekarar 2014, an yi amfani da masarautar wajen gudanar da mabanbantan ra’ayoyi don kalubalantar shugabancin Goodluck Jonathan.

A karshen shekarar 2025, an yi fatan cewa rikicin zai kawo karshe bayan Gwamna Abba Yusuf ya sauya sheka daga jam’iyyar Kwankwaso zuwa na Tinubu, wanda ya sanya shi cikin rukuni daya da Ganduje.Bayan shiga jam’iyyar gwamnati, Yusuf ya bayyana cewa ba shi da shirin cire Sanusi. Yayin da Sanusi da Yusuf sun auri ’yan’uwan Bayero.

LABARAI MASU NASABA

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba

Rahotannin sun nuna cewa wasu bangarorin siyasa a cikin APC mai mulki a Kano, ciki har da bangaren Yusuf da Ganduje, sun yi watsi da duk wani yukuri ya kiran Bayero a matsayin Sarkin Kano.

Domin hada kowane bangare cikin APC, an ce bangaren Ganduje ya kafa wasu sharudda ga Yusuf. Wani bangare na sharadin shi ne, zabi tsakanin mataimakin gwamna domin maye gurbin Aminu Abdulsalam wanda ya yi murabus, saboda biyayya ga Kwankwaso, ko kuma zabi wanda zai zama Sarkin Kano.A ranar 27 ga Afrilu, an tabbatar da Murtala Sule Garo, mai biyayya ga Ganduje, a matsayin mataimakin gwamna ga majalisar jihar, sannan daga baya aka rantsar da shi ya shiga ofis.Babu wasu rahotanni da ke cewa Tinubu ya tuntubi Bayero ko ya nuna goyon baya a tsakanin bangarorin APC a Kano. Dukkan Sanusi da Bayero makomansu na ga hannun ‘yan siyasa. Dole daya daga cikinsu ne za a amince da shi a matsayin Sarkin Kano

Bayero
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka
  • Sulaiman
    Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi
  • Sulaiman
    An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”
  • Sulaiman
    Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9
Bayero
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa

MASU ALAKA

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi
Ra'ayinmu

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

July 10, 2026
Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba
Ra'ayinmu

Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba

July 3, 2026
sikila
Ra'ayinmu

Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya

June 26, 2026
Next Post
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

July 27, 2026
Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026
Bayero

WAFU B 2026: Nijeriya Ta Doke Ghana Da Ci 4-2 A Wasan Farko

July 27, 2026
An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

July 27, 2026
Bayero

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

July 27, 2026
Bayero

Obi-Kwankwaso Obasanjo Yake Goyon Baya, Amma Atiku Zai Iya Lashe Zabe – Momodu

July 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana

July 27, 2026
Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil

Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil

July 27, 2026
Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano

Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano

July 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.