Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa tashin farashin gas ɗin girki (LPG) da ake fama da shi a halin yanzu ya samo asali ne daga rashin daidaiton canjin kuɗaɗen waje, tsadar sufuri da sauran matsalolin kasuwa, tare da umartar Hukumar Kula da Harkokin Mai ta Tsakiya da Ƙasa (NMDPRA) da ta ƙara sa ido domin tabbatar da daidaiton samar da gas a ƙasa.
Ƙaramin Ministan Albarkatun Man Fetur mai kula da harkokin Gas, Ekperikpe Ekpo, ya ce gwamnati ta fahimci damuwar jama’a kan ƙarin kuɗin gas ɗin girkin, amma ta ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da samar da isasshen gas mai sauƙin samu da araha ga gidaje, masana’antu da bangaren samar da wutar lantarki.
A cikin wata sanarwa da kakakinsa, Louis Ibah, ya sanya wa hannu ranar Litinin, ministan ya ce:“Sabbin sauye-sauyen farashin sun samo asali ne daga yanayin kasuwa ta yanzu, kamar rashin tabbas a farashin canjin kuɗaɗen waje, ƙarin kuɗin sufuri, da sauye-sauyen farashin LPG a kasuwannin duniya. Bai kamata a ɗauki waɗannan matsaloli a matsayin gazawar manufofin gwamnati ba.”
Bincike ya nuna cewa zuwa watan Yunin 2026, matsakaicin farashin gas ɗin girki ya kai kusan Naira 2,050 kan kowace kilo, idan aka kwatanta da kusan Naira 1,450 a farkon shekarar, lamarin da ya ƙara nauyi ga iyalai da dama a faɗin ƙasar nan.
Gwamnatin ta kuma umarci NMDPRA da ta ƙarfafa sa ido kan harkar domin tabbatar da wadataccen gas a kasuwa da rage matsalolin da ke haddasa hauhawar farashi.















Discussion about this post