• English
  • Business News
Thursday, May 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

by Sadiq
4 weeks ago
in Labarai
0
Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Aƙalla mutane 12 ne ‘yan ta’adda da ake zargin ‘yan Boko Haram ne suka kashe a ƙaramar hukumar Gwoza a Jihar Borno.

Mai Martaba Sarkin Gwoza, Alhaji Mohammed Shehu Timta, ya shaida wa LEADERSHIP cewa ‘yan ƙungiyar sa-kai na Civilian Joint Task Force (CJTF) guda biyu sun rasa ransu a harin kwanton-ɓauna a kan hanyar Kirawa a ranar Juma’a, 25 ga watan Afrilu, 2025.

  • Yadda Sakamakon Jawo Jarin Waje A Rubu’in Farko Na Bana Ya Ba Da Sha’awa A Kasar Sin
  • Zulum Ya Nuna Damuwa Kan Yadda Boko Haram Ke Dawowa Wasu Yankuna A Borno

A ranar Asabar, 26 ga watan Afrilu, wasu mutane 10 da suka je yin itacen girki a daji an kashe su a ƙauyen Bokko Ghide.

Wasu biyu kuma sun ji rauni sosai a harin.

Sarkin ya bayyana takaicinsa kan yawaitar hare-hare, yana mai cewa hakan na iya kawo cikas ga ƙoƙarin da gwamnatin Jihar Borno da sojoji ke yi na sake gina yankuna da kuma dawo da ‘yan gudun hijira gida.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5

Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn

“Abin takaici ne ganin yadda jami’an CJTF biyu da aka kashe a ranar Juma’a, sannan kuma wasu mutane 10 da suka je daji neman itace aka kashe su yau.

“Mun riga mun birne mamatan kamar yadda addinin Musulunci ya tanada, kuma an kwashe waɗanda suka ji rauni zuwa Maiduguri domin nema musu kulawar likitoci,” in ji Sarkin.

Ya yi addu’a Allah ya jiƙan mamatan ya kuma bai wa waɗanda suka jikkata lafiya.

Sarkin ya yaba wa gwamnati da sojoji bisa ƙoƙarinsu amma ya buƙaci a ƙara amfani da sabbin fasahohin zamani da kayan yaki masu ƙarfi domin yaƙar ‘yan ta’addan.

Ya yi gargaɗin cewa waɗannan hare-hare na iya tsoratar da manoma wajen komawa gonakinsu yayin da lokacin shuka ke gabatowa.

A wani ɓangare kuma, Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya sake kira ga rundunar soji da su ɗauki mataki wajen fatattakar ‘yan Boko Haram daga maɓoyarsu.

Gwamna Zulum ya yi wannan kira ne yayin da ya karɓi baƙuncin tawagar Gwamnatin Tarayya da suka haɗa da Ministan Tsaro, Mohammed Badaru Abubakar, da sauran manyan hafsoshin soji a gidan gwamnatin jihar da ke Maiduguri.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Boko HaramBornoHari
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Sakamakon Jawo Jarin Waje A Rubu’in Farko Na Bana Ya Ba Da Sha’awa A Kasar Sin

Next Post

Muhimman Dalilan Kirkiro Da Shirin Inganta Aikin Noma ‘SAPZ’

Related

‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5
Labarai

‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5

5 hours ago
Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn
Labarai

Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn

5 hours ago
Shirye-shiryen Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista
Labarai

Shirye-shiryen Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista

6 hours ago
Sabbin Ministoci
Labarai

Boko Haram: Majalisar Dattijai Ta Amince Da Kafa Sansanin Sojoji A Hong Ta Jihar Adamawa

7 hours ago
Rashin Tsaro: Matasa Sun Yi Zanga-zangar Toshe Babbar Hanya Saboda Satar Mutane A Edo
Labarai

Rashin Tsaro: Matasa Sun Yi Zanga-zangar Toshe Babbar Hanya Saboda Satar Mutane A Edo

9 hours ago
zulum
Labarai

‘Yan Ta’adda Na Amfani Da Sojoji Da ‘Yan Siyasa Wajen Samun Bayanan Sirri – Zulum 

10 hours ago
Next Post
Sin Ta Gina Cibiyoyin Fasahar Aikin Gona Na Gwaji Guda 24 A Afirka

Muhimman Dalilan Kirkiro Da Shirin Inganta Aikin Noma ‘SAPZ’

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5

‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5

May 21, 2025
Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan

Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan

May 21, 2025
Farar Dabarar Da Tsoffin Masana’antu Ke Yi A Kasar Sin Don Tafiya Da Zamani

Farar Dabarar Da Tsoffin Masana’antu Ke Yi A Kasar Sin Don Tafiya Da Zamani

May 21, 2025
Tottenham Ta Doke Manchester United A Wasan Karshe Na Europa 

Tottenham Ta Doke Manchester United A Wasan Karshe Na Europa 

May 21, 2025
Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn

Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn

May 21, 2025
Shirye-shiryen Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista

Shirye-shiryen Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista

May 21, 2025
Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka

Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka

May 21, 2025
Sin Tana Da Karfi Wajen Tinkarar Hadari Da Kalubale A Fannoni Daban Daban

Sin Tana Da Karfi Wajen Tinkarar Hadari Da Kalubale A Fannoni Daban Daban

May 21, 2025
Sabbin Ministoci

Boko Haram: Majalisar Dattijai Ta Amince Da Kafa Sansanin Sojoji A Hong Ta Jihar Adamawa

May 21, 2025
Sin Ta Soki Yunkurin Amurka Na Hana Amfani Da Chips Kirar Kasar Sin

Sin Ta Soki Yunkurin Amurka Na Hana Amfani Da Chips Kirar Kasar Sin

May 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.