ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

by Sani Anwar
1 hour ago
Talauci

Asusun ba da lamuni na duniya (IMF), ya bayyana cewa; duk da sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatin Nijeriya ta yi cikin shekara uku da suka gabata, fatara da karancin abinci sun kara karuwa a fadin kasar, inda kashi 63 cikin 100 na ‘yan Nijeriya ke fama da talauci a halin yanzu.

Asusun ba da lamuni na duniya (IMF), a cikin wani rahotonsa na 2026, na shawarwari kan Nijeriya da aka fitar a ranar Talata, ya ce; kimanin ‘yan Nijeriya miliyan 27 ne suka fuskanci matsalar karancin abinci a karshen shekarar 2025, duk da cewa; kasar ta samu karin tattalin arziki mai karfi da inganta asusun ajiyar waje da kuma sabunta kwarin gwiwar masu zuba jari.

A cewar asusun, gyare-gyaren da suka hada da kawar da tallafin man fetur, sassaucin ra’ayi na musayar kudi, tsauraran manufofin kudi da kuma kawo karshen gibin kudaden shiga, sun karfafa kwanciyar hankali a fannin tattalin arziki da kuma inganta karfin tattalin arzikin.

ADVERTISEMENT

“Karfafa wadannan gyare-gyare a cikin shekaru ukun da suka gabata, ya samar da ingantattun sakamako na tattalin arziki da kuma karfafa karfin gwiwa. Duk da haka, ‘yan Nijeriya da dama na ci gaba da shan wahala matuka,” in ji IMF.

Rahoton ya yi nuni da cewa, yayin da tattalin arzikin Nijeriya ya karu da kashi hudu cikin 100 a shekarar 2025, sannan kuma ana hasashen zai tashi kadan zuwa kashi 4.1 cikin 100 a shekarar 2026, hauhawar farashin man fetur da abinci da taki a duniya na kara tabarbarewar hauhawar farashin kayayyaki da kuma kara wahalhalu a tsakanin ‘yan kasar.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Habakar hauhawar farashin kayayyaki da ta yi kasa sama da shekara guda, ta haura zuwa kashi 15.4 cikin dari a cikin Maris din 2026, biyo bayan hauhawar farashin abinci da man fetur na duniya.

IMF ta yi gargadin cewa, yanayin duniya a halin yanzu, musamman yakin da ake yi a Gabas ta Tsakiya, na haifar da sabon hadari ga hasashen tattalin arzikin Nijeriya ta hanyar tsadar sufuri, abinci da makamashi.

Duk da haka, ta amince da ci gaba a cikin asusun ajiyar waje na Nijeriya, yana nuna cewa; babban asusun ajiyar kudi na duniya, ya tashi daga dala biliyan 40 a karshen 2024 zuwa dala biliyan 46 a 2025, yayin da asusun ajiyar kudi na duniya ya karu daga dala biliyan 23 zuwa dala biliyan 35 a lokaci guda.

Asusun ya kuma bayyana cewa, naira ta kara daraja da kashi 10 cikin 100, duk shekara idan aka kwatanta da dalar Amurka a watan Maris na 2026.

Duk da wadannan nasarorin da aka samu, IMF ta nuna damuwarta kan matsayin kasafin kudin Nijeriya, inda ta yi nuni da cewa; gibin gwamnati ya karu da kashi 4.4 a shekarar 2025 daga kashi 2.4 cikin 100 a shekarar 2024.

Ta kara da cewa, kudaden shigar da ake samu daga man fetir, bai yi kasa a gwiwa ba wajen hasashen kasafin kudin, yayin da kudaden ruwa na gwamnati ya cinye kashi 53 na kudaden shiga na tarayya a shekarar 2025, sama da kashi 41 cikin 100 na bara.

Rahoton ya kara nuna damuwa game da kashe kudaden da ba a cikin kasafin kudi suke ba, inda ya bukaci hukumomi da su karfafa gaskiya, rikon amana da tsarin gudanar da hada-hadar kudi.

“’Yan Nijeriya da dama na ci gaba da wahala, inda talauci da karancin abinci zai iya ta’azzara rayuwarsu,” in ji Hukumar ta IMF bayan kammala shawarwari da hukumomin Nijeriya.

Asusun ya kuma bukaci gwamnatin tarayya, ta ci gaba da kasancewa tsaka-tsaki kan kasafin kudi na shekarar 2026, tare da kare fifiko da ciyar da al’umma gaba.

Ta kuma shawarci gwamnati, da ta kara inganta shirye-shiryen musayar kudi da za ta taimaka wa ‘yan Nijeriya, musamman masu rauni.

A cewar rahoton, a halin yanzu gidaje miliyan 9.2 ne kawai suka shiga cikin tsarin musayar kudade na gwamnati a kan magidanta miliyan 15, wadanda suka ci gajiyar tallafin, sun samu akalla naira 25,000, tun daga shekarar 2023.

IMF ta kuma yi kira ga Babban Bankin Nijeriya (CBN), da ya ci gaba da tsare-tsaren hada-hadar kudi, har sai an shawo kan hauhawar farashin kayayyaki da kuma hasashen hauhawar farashin kayayyakin.

Asusun ya kuma yaba wa babban bankin, bisa ci gaban da aka samu wajen nusar da hauhawar farashin kayayyaki da kuma kiyaye tsarin canji.

A bangaren hada-hadar kudi kuwa, IMF ya bayyana cewa; bankuna 33 a cikin 37 na Nijeriya, sun cika sharuddan sake fasalin kudi a wa’adin watan Maris na 2026, yayin da har yanzu bankuna hudu ke ci gaba da tafiyar da harkokin shari’a.

Duk da haka, ta yi gargadin cewa; bashin da ba a biya ba, ya karu da kashi takwas a cikin rubu’in 2025.

Asusun na IMF, ya kuma bukaci hukumomin Nijeriya da su hanzarta yin gyare-gyare a fannin wutar lantarki, samar da ababen more rayuwa, noma da kuma bunkasar jarin Dan’adam, domin samar da ci gaban da zai habaka tattalin arziki.

Kazalika, ya jaddada cewa; rashin tsaro ya kasance wata babbar barazana ga zuba jari, noma da kuma hako mai a fadin kasar.

Rahoton ya kara da cewa, zaben shugaban kasar Nijeriya da aka shirya gudanarwa a watan Janairun shekarar 2027, zai iya haifar da karin kasada a kasafin kudi, idan aka samu raguwar garambawul ko kuma matsin tattalin arziki ya karu gabanin zaben.

Talauci
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tinubu Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Kan Jajircewarsu Wajen Kawo Karshen Ta’addanci
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno

MASU ALAKA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya
Rahotonni

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri
Rahotonni

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Next Post
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.