Kamfanin BUA ya musanta rahotannin da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa shugaban kamfanin, Abdul Samad Rabiu, na shirin sayen kaso 70 cikin 100 na ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars.
A cikin wata sanarwa da kamfanin ya fitar a ranar Litinin, BUA ya ce labarin ba gaskiya ba ne, kuma bai fito daga kamfanin ko shugaban kamfanin ba.
Sanarwar ta bayyana cewa babu wani tayi ko yarjejeniya da aka yi tsakanin BUA da Kano Pillars kan batun sayen hannun jari a ƙungiyar.
Kamfanin ya kuma ce har yanzu babu wata tattaunawa da aka yi tsakanin ɓangarorin biyu kan wannan batu.
BUA ya buƙaci jama’a da kafafen yaɗa labarai da su yi watsi da rahoton, tare da bin bayanan da kamfanin ke fitarwa ta sahihan kafafen sadarwarsa.














