Da misalin karfe 5:13 na sanyin safiyar jiya Litinin, ’yan sama jannatin Shenzhou 21 suka bude kofar tashar binciken sararin samaniya ta Sin, domin maraba da ’yan sama jannatin kumbon Shenzhou-23, wannan shi ne karo na 8 da ’yan sama jannatin kasar Sin suka hadu a sararin samaniya.
Wani babban batu shi ne yadda a karon farko, ’yar sama jannati daga yankin Hong Kong na Sin watau Li Jiaying, da ake kira Lai Ka-ying, ta shiga tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin.A ganina, wannan gagarumin lamarin da ya watsa wa masu bata sunan kasar Sin kasa a ido, domin ya tabbatar da manufar nan ta “kasa daya mai tsarin mulkin biyu.” Duk da cewa yankin Hong Kong na kasar Sin, yanki ne na musamman mai cin gashin kansa, to yana karkashin babban yankin Sin, kuma Sin na shigar da shi cikin harkokin da suka shafi ci gaban kasa da na al’umma domin samun moriya da makoma ta bai daya ba tare da mayar da wane bangare saniyar ware ba.
Yadda matashiya daga yankin ta shiga cikin aikin na sama jannati, ya sake tabbatar da burin al’ummar Sinawa na ganin dunkulewar kasarsu wuri guda, ya tabbatar cewa, masu neman ta da zaune tsaye ne ke ingiza ’yan aware. Baya ga ’yar sama jannati daga yankin Hong Kong, a ranar 22 ga watan Afrilun bana, kasar Sin ta sanar da cewa an zabi wasu ’yan kasar Pakistan biyu a matsayin ’yan sama jannati na kasar waje na farko, da za su karbi horo domin shiga aikin binciken samaniya na Sin.
An ce Muhammad Zeeshan Ali da Khurram Daud, za su karbi horo a kasar Sin, kuma bayan sun kammala horo da tantancewa, daya daga cikinsu zai shiga cikin tawagar masu aikin binciken samaniya na Sin, inda zai zama dan sama jannati na farko na kasar waje da zai shiga tashar Tiangong ta kasar Sin.
Watau wannan ya kara bayyana ma’anar manufar bude kofa ta Sin, inda yake nuna cewa, ba kawai ga kasuwanci ko bude ido kasar Sin ke bude kofarta ba, tana budewa ne ta kowane bangare domin samun ci gaba na bai daya.
Hakika wannan na zaman gagarumar nasarar hadin gwiwar kasa da kasa a fannin binciken samaniya ta Sin. Wannan ya tuna min da wata ’yar Nijeriya, Dr. Olusola Ashiru wadda kasar Sin ta ba ta damar shiga aikin nutso domin bincike a karkashin teku a shekarar 2024. Kafin sannan ta ce ba ta taba samun wannan dama ba, inda take dogoro da ayyukan wasu wajen koyar da dalibanta.
Dukkan wadannan yunkuri na kasar Sin na kara bayyana ra’ayi da kuduri da burinta na bude kofa da musayar ilimi da hadin gwiwa domin samun moriyar juna.
Bisa gayyatar karin bangarori da kasashe domin hadin gwiwar gudanar da binciken kimiyya, za a gaggauta samun ilimi da fahimtar abubuwa masu sarkakiya da inganta kare duniya da kuma samun ci gaba da moriya na bai daya, wandanda za su kai ga samar da al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post