ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bude Kofa Ta Kowace Fuska Wata Hanya Ce Ta Samun Makoma Ta Bai Daya

by Sulaiman and CGTN Hausa
4 weeks ago

Da misalin karfe 5:13 na sanyin safiyar jiya Litinin, ’yan sama jannatin Shenzhou 21 suka bude kofar tashar binciken sararin samaniya ta Sin, domin maraba da ’yan sama jannatin kumbon Shenzhou-23, wannan shi ne karo na 8 da ’yan sama jannatin kasar Sin suka hadu a sararin samaniya.

Wani babban batu shi ne yadda a karon farko, ’yar sama jannati daga yankin Hong Kong na Sin watau Li Jiaying, da ake kira Lai Ka-ying, ta shiga tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin.A ganina, wannan gagarumin lamarin da ya watsa wa masu bata sunan kasar Sin kasa a ido, domin ya tabbatar da manufar nan ta “kasa daya mai tsarin mulkin biyu.” Duk da cewa yankin Hong Kong na kasar Sin, yanki ne na musamman mai cin gashin kansa, to yana karkashin babban yankin Sin, kuma Sin na shigar da shi cikin harkokin da suka shafi ci gaban kasa da na al’umma domin samun moriya da makoma ta bai daya ba tare da mayar da wane bangare saniyar ware ba.

Yadda matashiya daga yankin ta shiga cikin aikin na sama jannati, ya sake tabbatar da burin al’ummar Sinawa na ganin dunkulewar kasarsu wuri guda, ya tabbatar cewa, masu neman ta da zaune tsaye ne ke ingiza ’yan aware. Baya ga ’yar sama jannati daga yankin Hong Kong, a ranar 22 ga watan Afrilun bana, kasar Sin ta sanar da cewa an zabi wasu ’yan kasar Pakistan biyu a matsayin ’yan sama jannati na kasar waje na farko, da za su karbi horo domin shiga aikin binciken samaniya na Sin.

ADVERTISEMENT

An ce Muhammad Zeeshan Ali da Khurram Daud, za su karbi horo a kasar Sin, kuma bayan sun kammala horo da tantancewa, daya daga cikinsu zai shiga cikin tawagar masu aikin binciken samaniya na Sin, inda zai zama dan sama jannati na farko na kasar waje da zai shiga tashar Tiangong ta kasar Sin.

Watau wannan ya kara bayyana ma’anar manufar bude kofa ta Sin, inda yake nuna cewa, ba kawai ga kasuwanci ko bude ido kasar Sin ke bude kofarta ba, tana budewa ne ta kowane bangare domin samun ci gaba na bai daya.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Hakika wannan na zaman gagarumar nasarar hadin gwiwar kasa da kasa a fannin binciken samaniya ta Sin. Wannan ya tuna min da wata ’yar Nijeriya, Dr. Olusola Ashiru wadda kasar Sin ta ba ta damar shiga aikin nutso domin bincike a karkashin teku a shekarar 2024. Kafin sannan ta ce ba ta taba samun wannan dama ba, inda take dogoro da ayyukan wasu wajen koyar da dalibanta.

Dukkan wadannan yunkuri na kasar Sin na kara bayyana ra’ayi da kuduri da burinta na bude kofa da musayar ilimi da hadin gwiwa domin samun moriyar juna.

Bisa gayyatar karin bangarori da kasashe domin hadin gwiwar gudanar da binciken kimiyya, za a gaggauta samun ilimi da fahimtar abubuwa masu sarkakiya da inganta kare duniya da kuma samun ci gaba da moriya na bai daya, wandanda za su kai ga samar da al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya. (Fa’iza Mustapha)

Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
  • Sulaiman
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • Sulaiman
    Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
  • Sulaiman
    Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

MASU ALAKA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
Daga Birnin Sin

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Next Post
Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.