ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Hukunta Masu Ba Da Bashi Ta Intanet Da Ke Cin Mutuncin Abokan Hulda

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
Bashi

Karuwar kafofin bayar da bashi na bogi a kafar sadarwar intanet a Nijeriya ya haifar da manyan matsaloli ga masu mu’amala da su. Yana da matukar muhimmanci a fahinci cewa, wadannan kafofi sun samu karin bunkasa ne a lokacin da aka fuskanci kulle ne hana zirga-zirga sakamakon annobar cutar Korona, abin da ya sa al’umma da dama suka zauna a gida cikin kunci na rashin kudi, a nan ne kafofin suka fito inda mutane da dama suka rungume su saboda suke da saukin ka’dojin bayar da basuka.

Ga ‘yan Nijeriya da dama, a wancan lokacin, al’amari ne da za a yi wa maraba, al’amarin da al’umma da dama suna runguma ganin ya zo a daidai lokacin da mutane ke cikin tsaka mai wuya na matsalar tattalin arziki da kuma zaman gida da annobar cutar korona ta haifar mana. Kamar dai sauran abubuwan da kan zo mana na alhairi, ana cikin haka ne sai bata gari suka shiga cikin harkar, daga nan abin da aka dauka a matsayin ceto sai ya zama tashin hankali da annoba da masu mu’amala da shi.

  • CBN Ya Ɗage Takunkunmin Zuba Adadin Dala 10,000 A Asusun Ajiya Na Kudaden Waje

Abin takaici a nan kuma shi ne yadda abin da aka dauka a matsayin lamarin da zai kawo sauki ga mutum sai gashi ya zama kafar da ake tozarta mutum tare da kulla masa sharri, musamman daga wasu shugabannin kafofin bayar da basukan. An sha samun abubuwan tashin hankali ga masu cin bashin inda a kan damu wasu mutane da kiran waya ana cewa, su tuntubi wanda ya ci bashi, da kuma karin sharrin cewa, wanda ya ci bashin yana dauke da cutar kanjamau da sauransu.

ADVERTISEMENT

Akwai labarin wani da ya ci bashin kudi a irin wadancan kafafen, inda suka wallafa sanarwar wai ya mutu, mutumin ya razana kwarai da ya ga sanarwar mutuwarsa tana yawo a kafafen sadarwa inda aka ce wai ya mutu ne a ranar 4 ga watan Janairu na shekarar 2022 kuma wai za a yi jana’izarsa a karshen watan. Wani shi ma da irin haka ta rutsa da shi, ya bayyana yadda wata kafar bayar da bashi ta wallafa hoton da sunansa a shafukan facebook.

Ire-iren wadannan cin mutuncin da kafafen bayar da bashi ta intanet ke yi wa al’umma na da yawan hgaske kuma ya kamata a gaggauata dakatar da su, ya kamata hukumomi su dauki matakan kawo karshen wadannan cin mutuncin da ake yi ba tare da bata lokaci ba. Muna jin dadin yadda gwamnatin tarayya ta hannun Hukumar Kare Masu Saye da Mu’amala da Cibiyoyi ((FCCPC) ta fara daukar tsatsaurar mataki a kan ire-iren wadanan kafofi.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

A tattaunawar da shugaban hukumar FCCPC, Babatunde Irukera, ya yi da ‘yan jarida kwanakin baya, ya jaddada kudurin hukumar na kulle duk wata kafar bayar da bashi ta intanet da ta dauki cin mutuncin masu mu’amala da ita ta hanyar yi musu sharri da sauran cin mutunci. Shirin hukumar na goge shafin duk wata kafar bayar da bashi da aka kama da laifin cin mutuncin masu mu’amala daga manhajar goggle zai zama babbar darasi ga sauran masu shirin fara irin wannan dabi’ar.

Ra’ayin wannan jaridar shi ne ya kamata dukkan kafafen bayar da bashi da suka rungumi cin mutuncin masu hulda da su su sani cewa, za su fuskanci hukuncin doka sakamakon ayyukansu na cin mutuncin masu mu’amala da su. Shugaban hukumar ya kara da cewa, a yayin da ake maraba da masu harkokinsu ba tare da karya doka ko cin mutunci mutane ba a kasar nan. Wadanda suka rungumi karya doka a matsayin sana’arsu za su dandana kudarsu.

Ta hanyar daukar mataki, Hukumar FCCPC ta dauki kare hakokin ‘yan Nijeriya masu hulda da hukumomi daban daban, wannan kuma abin a yaba ne. Bai kamata a shiga tozarta masu neman cin bashi ta hanyar aika sakonnin karta ta kwana don cin mutuncin su ba, yana da matukar muhimmanci hukumomi su shigo don tsaftace harkokin kafofin bayar da basuka ta intanet tare da samar da dokokin da za su yi aiki da su don kauce wa wuce gona da iri.
Tabbas barazanar da hukumar FCCPC ta yi na goge manhajar duk wata kafar bayar da bashin da aka samu da laifi daga GOOGLE zai taimaka wajen tsaftace hakar ta yadda da mai bayar da bashin da kuma masu karbar za su yi mu’amala cikin mutuntunta juna.

Yana da matukar muhimmanci a fahinci cewa, mutanen da suke shiga matsala wajen biyan bashin da suka ci, mutane ne da suke fuskantar matsalar tattalin arziki na gaskiya, a kan haka suke garzayawa wajen masu bayar da irin wadannan basukan don neman ceto, saboda haka bai kamata a yi amfani da wannan damar ba wajen ci musu mutunci, irin haka zai kara jefa su cikin hali na damuwa da zai kuma iya jefa su cikin matsalar da ba za a iya sanin yadda za ta kare ba.

Ya kuma kamata a kara kaimi wajen wayar da kan al’umma musamman ma masu mu’amala da kafafen bayar da bashi ta intanet a kan hakokinsu, a kuma samar da hanyar da za su iya kai kokarafi a kan duk wani cin mutunci da aka yi musu a yayin da suke karbi bashi.

Hukumar FCCPC na iya samar da kafar aiki tare da masu ruwa da tsaki don sanya ido a kan ayyukan ire-iren kafofin bayar da bashi ta intanet masu cin mutuncin masu hulda da su.

Bashi
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano
Siyasa

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

April 25, 2026
Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

March 18, 2025
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

November 10, 2024
Next Post
Matan Nijeriya Sun Buga Canjaras Da Kasar Canada A Wasan Farko Na Gasar Cin Kofin Duniya

Matan Nijeriya Sun Buga Canjaras Da Kasar Canada A Wasan Farko Na Gasar Cin Kofin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.