ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Magance Yawaitar Hatsarin Jirgin Kasa A Nijeriya

by Leadership Hausa
3 years ago
Jirgin Kasa

A kwanakin baya ne aka tabbatar da mutuwar mutum 6 yayin da wasu dama suka ji raunuka a wani taho-mu-gama da jirgin kasa da motar ma’aikatan (BRT) ta yi a yankin Shogunle da ke Ikeja, a Jihar Legas.

Rahottani sun nuna cewa, motar na kokarin tsallake hanyar jirgin ne daidai lokacin da jigin ke shigowa inda jirgin ya yi karo da motar ya kuma tafi da ita daga tashar PWD har zuwa tashar Shogunle, tafiyar4 kusan nisan mita fiye da 100.

  • ‘Yan Nijeriya Sama Da Mutane 39 Ne Suka Mutu A Zaben 2023
  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Daina Muzgunawa Kamfanonin Waje

Idan kuma za a iya tunawa, a watan Disamba ne na shekarar da ta gabata jirgin kasa dauke da mutane da ya taso daga Abuja zuwa Kaduna ya yi karo da motar wata mata inda anan take ta ce ga garinku nan, hatsarin ya faru ne a daidai unguwar Chikakore da ke yankin Kubwa a yankin babbar birnin tarayya Abuja.

ADVERTISEMENT

Haka kuma a watan Janairu wani jirgin da ya taso daga Kaduna zuwa Abuja ya kauce wa hanya a Abuja sai dai cikin ikon Allah babu wanda ya rasa ransa a hatsarin.

Ba zai yiwu mu manta a cikin sauri ba harin da ‘yan ta’adda suka kai wa jirgin kasa a jihohin Kaduna da Edo ba a cikin watannin 12 da suka wuce, inda har aka kai ga rasa rayukanh mutane da dama, baya ga mutanen da aka yi garkuwa da su, lallai bai kamata irin wannan ya sake faruwa ba.

LABARAI MASU NASABA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

A ra’ayin wannan jaridar, aukuwar hatsarin da aka samu a na baya-bayan na a Jihar Legas da Abuja sun bayyana bukatar a yi maganin matsalar tare da daukar mataki na kawo karshen yawaitar hatsarin da ke tattare da sufurin jirgin kasan Nijeriya. A bayyana yake cewa, ana bukatar a tabbatar da daukar matakan da suka kamata don kare aukuwar ire-iren wannan hatsaruran a nan gaba.

Wadanna hatsuran suna kara fito da manyan matsalolin da bangaren sufurin jiragen kasan Nijeriya ke fuskanta ne, kuma da bukatar a gaggauta daukar matakin kawo karshen su.

Kafin wannan gwamnatin ta dauki matakin farfado da sashin sufurin jirgin kasa, bangaren ya yi fama da rashin kulawa na tsawon shekaru masu yawa daga gwamnatocin da suka gabata.

Domin ganin an kawo karshe ko rage hatsarin jingin kasa da ake samu a Nijeriya akwai bukatar masu ruwa da tsaki su gaggauta daukar matakin ganin an warware matsalolin da sashin ke fuskanta.

A ra’ayinmu akwai bukatar da a samar wa tsarin jirgin kasan Nijeriya cikkaken kayan aiki na zamani tare da daga darajar wadanda ake da su a halin yanzu. Dole gwamnati ta zuba manyan jari a kokarin samar da kayan aiki na zamani. Wannan ne zai tabbatar da jiragen za su iya yin gudu tare da kuma rage aukuwar hatsurar da ake samu a kai-kai.

Haka kuma yakamata a rika sanya tare da kula da kayyakin aiki. Ya kuma kamata gwamnati ta zuba jari wajen horar da ma’aikata don su samu sanin makaman aiki da sabbin  na’urorin da ke shigo da su.

Muna kuma bayar da shawarar da a samar da wasu ka’idoji na tabbatar da kariya a harkar tafiyar da safarar jiragen kasa. Dole ne kuma hukumomi su tsayu don ganin ana aiki da dokokin da aka samar ta hanyar amfani da kwararrun ma’aikatan da ake da su.

Akwai kuma bukatar a inganta kafafen sadarwa a tsakanin direban jiragen da cibiyar da ke bayar da umarnin zirga-zirgan don kare aukuwar hatsari. Dole gwamnati ta zuba isashen jari a kayayyakin sadarwa na zamani ta yadda za a iya sanar da direban jirgi halin da hanyoyin dogo ke cik don kare aukuwar hatsari.

A wani bangaren kuma al’ummar Nijeriya da dama basu san ka’doji da alamomin hanyar jirigi ba saboda yadda aika yi watsi da bangaren na tsawon lokaci. Dole gwamnati ta farfado ta hanyar gangami na musamman na fadakar da al’umma a kan irin munin da ke tattare da hatsarin jirgin kasa.

Wannan zai tabbatar da cewa al’umma na sane da irin hatsarin da ke tare da tsallake hanyar jirgin kasa tare da kuma daukar matakin kariya da kuma bin dokokin da aka shimfida.

Bayan wadannan matakan da muka zayyana, akwai kuma bukatar gwamnati ta hada hannu da kamfanoni masu zaman kansu don suma su zuba jari a harkar sufurin jirgn kasa. Shigo ga kamfanoni masu zaman kansu zai taimaka wajen bunkasa bangaren zai kuma kara inganta tsaro da yadda ake gudanar da bangaren gaba daya.

Ba tare da wani kokwanto ba, yawancin hatsarin da ake samu yana faruwa ne sakamakon sakaci na dan adam, kuma gashi har yanzu ba aji labarin an hukunta wani ko wata ba. Kamar yadda muka sha fada laifuka na cigaba da bunkasa a Nijeriya ne saboda ba a kai ga hukunta masu aikata laifin.

Hatsarin jirgin da ya auku na baya-baya nan a Legas da Abuja ya kamata su zama sun zaburar da gwamnatin tarayya da hukumar kula da jiragen kasa a Nijeriya a kan bukatar da samar da cikakken kulawa ga hanyoyin jiragen kasa.

Mun yi imanin cewa, inhar aka yi amfani da wadannan shawarwarin za a samu raguwar hatsarin jiragen kasa a Nijeriya.

Jirgin Kasa
Leadership Hausa
+ postsBio
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    “Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

MASU ALAKA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

June 3, 2026
Next Post
Matasan Da Za A Dama Da Su A Sabuwar Gwamnati

Matasan Da Za A Dama Da Su A Sabuwar Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.