A yau Juma’a mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning, ta ce sashen masana’antu masu nasaba da aikin soji na kasar Japan da a yanzu ke kara fadada cikin sauri, ya shaida wani babban ci gaba a aniyar kasar ta gaggauta maido da karfin soji, tare da haifar da matukar damuwa ga sassa daban daban.
Mao Ning, ta ce “Ya kamata daukacin al’ummun duniya masu burin zaman lafiya ciki har da Japanawa, su zamo masu zura ido, domin tabbatar da dakile yiwuwar Japan ta sake maimaita tarihin fadada karfin soji”. Ta ce Sin na kira da babbar murya ga masu tsattsauran ra’ayi na Japan, da su saurari muryoyin adalci, su kauracewa hawa turbar da ba ta bullewa, ta farfado da karfin soji.
Mao, ta yi wannan kira ne yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa, lokacin da aka nemi ta yi tsokaci dangane taron karawa juna sani, albarkacin cika shekaru 80 da bude shari’un birnin Tokyo, wanda jami’ar Shanghai Jiao Tong, da dakin tunawa da wadanda suka mutu cikin kisan kiyashin birnin Nanjing da dakarun mamaya na Japan suka yi, suka shirya cikin hadin gwiwa a jiya Alhamis zuwa yau Juma’a a birnin Shanghai. (Saminu Alhassan)














Discussion about this post