Kamfanin Ciminti na Ɗangote, ya ƙaddamar da shirye-shiryen jin ƙaai ga alummar jihar Biniwe na miliyoyin Naira.
Akasarin waɗanda za su amfana, sun kaance manoma, mata da kuma matasa, da suka fito daga alumomin shida, na ƙaramar hukumar Gboko.
Yankuna da za su amfana su ne, Tse-Kucha, Ƙuarry, Amua, Mbazembe, Mbatur da kuma na Pass Brothers.
Mata 150, a ƙarƙashin, za su karɓi tallafin kuɗi, domin ƙara bunƙasa sana’oinsu, ida kuma manoma, 52, za a rabar masu da kayan aikin noma, tare da kuma horas da matasa 30, kan koyon sana’oin hannu.
A jawabinsa a wajen ƙaddamawar, Ministan Bunƙasa Albaraktun Ƙasa Dakta Dele Alake, ya yabawa rukunonin kamfanin na Ɗangote, kan wannan tagomashin, ga yankunan da suka amafa.
Alake, wanda ya samu wakilcin Madam Usman Adijatu, a wajen taron ya ce, Gwamnatin Tarayya, na alfahari ci gaba da gudunmawar da kamfanin na Ɗangote ke yi, a jihar da kuma ɗaukacin faɗin ƙasar.
A cewarsa, wannan aikin na tallawar, da kamfanin ke ci gaba da yi, tamkar, marawa Gwamnatin Tarayya baya ne, kan ƙoarin da take ci gaba da yi, na rage talauci da inganta rayuwar ‘ayn ƙasar, musamman a yankunan da ake da ma’adanan ƙasa da masana’antu.
Alake, ya yi kira ga waɗanda suka amfana da tagomashin, da su yi amfani da su, yadda ya kamata.
Shi kuwa, shugaban ƙasashen gudanawar ta shiyyar Afirka na kamfanin na simitin Mista Wakeel Olayiwola, ya jaddada ci gaba da mayar da hankali, na kamfanin, na intnata rayuwar alumma a ƙarƙashin shirinsa na jin ƙai, wato CSR.
Ya kuma danganta alumomin da ke a yankin, a matsayin masu son zaman lafiya da bayar da goyon bayansu na nuna dangantaka.
Ya buƙace su, kar su yi ƙasa a gwaiwa, wajen ci gaba da nuna wannan ɗabi’ar ta su, ta gari.















Discussion about this post