Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar a yau Juma’a cewa, bunkasar kasar Sin ba ta kawo barazana ga kowane bangare ba, kuma hakan na sa kaimi ga sassan kasa da kasa wajen samun ci gaba tare.
Ya ce kirkire-kirkire da karfin samar da kaya na kamfanonin kasar Sin, ba za su kawo matsin lamba ga duniya ba, amma ra’ayin ba da kariya ga cinikayya mai kafa shinge, da yanke hulda shi ne ya haifar da illa ga duniya.
A kwanakin baya ne, mujallar Time ta kasar Amurka, ta gabatar da jerin sunayen kamfanonin fasahar AI mafi muhimmanci guda 10 na shekarar 2026, inda kamfaonin Sin guda uku suka kasance cikin jerin. Game da hakan, kakakin ya yi nuni da cewa, kamata ya yi bunkasar kimiyya da fasaha su kawo moriya ga dukkanin dan Adam, domin kuwa sashen da ya yi watsi da saura zai haifar da illa ga kansa.
Game da batun shirin kungiyar EU na kafa dokar hana kamfanonin Sin su shiga aikin gina ayyukan more rayuwa a nahiyar Turai, Lin Jian ya yi fatan bangaren EUn zai kiyaye dangantakar tattalin arziki, da cinikayya a tsakaninsa da Sin yadda ya kamata, kana ya dakatar da haifar da illa ga raya dangantakarsu.
Game da matakin gwamnatin Birtaniya, na kamawa, da mika ‘yan kasar Sin su biyu gaban wata kotu dake Birtaniyar, Lin Jian ya yi nuni da cewa, wannan wani yunkurin siyasa ne, kuma kasar Sin ta yi Allah wadai da hakan, ta kuma tuntubi bangaren Birtaniya domin neman daidaita batun. (Zainab Zhang)















Discussion about this post