Hukumar rabar da tattalin arzikin kasa ta yi gargadin cewa, Nijeriya za ta iya tabka asarar samun damar masu zuba hannun jari a cikin tattalin arzikin kasar, matukar ta gaza yin gaggawar yin rijitar yan kasuwa.
Shugaban kwamitin sanya ido kan zuba hannun jari na hukumar Enefe Ekene ne, yayi wannan gargadin a wata ganawa a ofishin ministar ma’aiktar masana’antu, kasuwanci da zuba hannun jari Dakta Jumoke Oduwole da ke Abuja.
A cewarsa, jinkirin da ake ci gaba da samu, wajen yin rjistara, musamman na kamfanonin da ke a kasar, hakan na kara dakile samun dama ga kasar, wajen yin gasa a bangaren zuba jari, na duniya.
Ya bukaci da gaggauta tabbatar da an yi sauye-sauye wadanda za su yi daidao da zuba jari na kasar nan wanda kuma zai kai, matsayi irin na fadin duniya, musamman a bangaren yin rijista da kuma janyo masu zuba jari.
Ya yi nuni da cewa, samun jinkiri, na sanya masu zuba jari, su gwamace sun kuma wasu kasashe domin su zuba jarinsu, inda can ake tuni, aka samar da ingantatun tsare-tsare, na zuba jari.
Tagwar ta kuma jaddada mahimmancin bukatar a taimaka wa masu zuba jari a fannin tattalin azrki, da ke a cikin kasar nan, tare da kuma kara inganta yadda ake fitar da kaya daga cikin kasar, zuwa ketare.
Da take na ta jawabin Dakta Jumoke, ta amince da wannan damuwar da kwamtin ya bijiro da ita, inda ta shedawa kwamtin cewa, a yanzu haka, ma’aikatarta, na kan samar da sauye-sauye da kara inganta ayyukan hukumomin gwamnatin kasar.















Discussion about this post