Lolaci ya yi da za a kawo ƙarshen yadda wasu marasa imani, a ƙasar nan, ke ɗaukar doka a hannun domin ɗaukar rayukan ƴan Nijeriya, alhali ba tare da sun aikata wani laifi ba.
Wannan batun, yazo dai dai da yadda a ranar 21 ga watan Yunin 2026, gungugun wasu fusatattun mutane, a kan hanyar Maraban Jos zuwa garin Zariya a jihar Kaduna, suka yiwa wata Malamar addinin Musulunci Malama Malama Ummulkhair, Usman Aliyu, kisan gilla, ta hanyar ƙone ta da ranta.
Mariganyiyar, mai ƴaƴa biyar, fusatattun mutanen, sun ƙone ta ne, bisa zargin wai, ta saci yara.
Wani ƙarin abin baƙin ciki shi ne, kisan gillar ba wai ya auku kai tsaye, a kan titi bane, domin baiwar Allah tuni an miƙa ta a ofishin ƴansanda, kan zargin satar yara, amma duk da haka, gungun marasa imanin suka yiwa ofishin na ƴansandan na Maraban Jos ƙawanya.
An yi zargin cewa, yawan gungun mutanen ne, ya sa suka fi ƙarfin jami’ian ƴansanda da ke a ofishin, wanda hakan ya tilasata su, miƙa matar ga fusatatun mutanen, inda su kuma suka ɗauki doka a hannun su, ta hanyar babbake ta, inda za a iya haka, ya nuna cewa, akwai gazawar samun bayanin sirri.
Kazalika, aukuwar wannan mummunan yanayi, ya nuna zahirance, na irin sakaci a ɓangaren mahukunta na kare rayuwar waɗanda suke mulka, musamman wanɗada ake tsare da su, a hannun su.
Bayanan da masu gani da ido, a lokacin da lamarin ya auku, musamman kan zargin da aka yiwa DPO ɗin ofishin, na cewa, shi da kansa ne, ya miƙa matar ga gungun fusatattun muatene da suka yi cirko-cirko a a wajen ofishin, ya nuna irin rashin iya ƙwarewar aiki, na ƴansanda.
Kazalika, duk da ankararwar da wani ganau a wajen ya yi, na cewa, miƙa matar ga mutanen, zai iya sanya ta rasa ranta, amma DPO ɗin, ya yi ƙememe da shawarar tata.
Haka zalika, ita wata mata a wajen ta yi ƙoƙarin shiga tsakani, amma mutanen suka yi barazar ƙona ta.
Waɗanan zarge-zargen, sun yi hannun Riga da iƙirarin da da DPO ɗin ya yi, na cewa, gungun mutanen sun yi yunƙurin nuna ƙarfin Tuwo, na kaɓar matar da tsiya.
A ɓangaren rundunar ƴansandan jihar ta kawai yi tir da aukuwar lamarin ne, tare da cafko mutane 24 tare da kuma kamo ƙarin wasu, da ake zargi, da aikata wannan halin na dabbacin tare.
Ya zama wajbi, a gaggauta gudanar da bincike, zargin rawar da DPO ɗin ya taka da kuma sauran jami’ansa, da ake zargi da hannun kan lamarin, indan an same su da laifi, a hukunta su, kamar yadda dokar ƙasa ta tana.
A ɓangaren mijinta Malam Muhammad Aliyu kuwa, ya bayyana cewa, bayan aukuwar lamarin, ƴaƴansu, sun ci gaba da tambayarasa, shin, ina Mamansu take.
Lamarin ya jefa rayuwar ɗansu mai shekaru 14, a cikin ƙuncin damuwa, tare da yawan furta sai ƙwatowa mahaifiarsu, haƙƙinta.
Ya zama wajibi, rundunar ƴansanda ta ƙasa, ta biya isashiya diyya ga iyalan mariganyiyar.
Gazawar da ƴansanda na rashin kare rauywar waɗanda suke tsare da su a ofis ɗinsu, hakan ne, bai wa ƴan Nijeriya damar, ɗaukar doka a hannun su, inda haka ke ci gaba da zama babar haɗari, musamman kan batun zargin satar yara.
Wannan lamarin zai kuma iya ci gaba da aukuwa, inda a wata rana, zai rkiɗe zuwa dabar siyasa, ko rikicin ƙabilanci, ko kuma addini, da sauran rikice-rikice.
Kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999 da aka sabunta, ya bai wa kowanne ɗan ƙasa, damar yin rayuwa da kare ƴancinsa.
Sai dai, abin baƙin cikin shi ne, Malama Ummulkhairi, ba ta samu wannan kariyar daga gun ƴansanda na kare ranta ba
Ƙungiyoyin addnin Musulunci da dama, kamar irinsu, MULAN, sun yi tir da aukuwar lamarin, tare da yin kira, da a gudanar da cikakken bincike.
Bugu da ƙari, ya zama wajibi, Gwamnatin Kaduna da rundunar ƴansanda ta ƙasa, su ɗauki matakan gaggawa, musamman domin a gudanar da cikakken bincike, tare da tabatar da an hukunta DPO ɗin da wasu jami’ansa, da ake zargi.
Ba za ci gaba da lamuntar yadda wasu ƴan Nijeriya ke ɗaukar doka hannun su ko kuma yiwa dokar karan tsaye, ba tare da wasu ƙwararan hujoji ba, bai kuma kama ace, Jinin Malama Ummulkhairi, ya tafi a banza ba.














