ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba

by Ra'ayinmu
1 day ago
Jos

Lolaci ya yi da za a kawo ƙarshen yadda wasu marasa imani, a ƙasar nan, ke ɗaukar doka a hannun domin ɗaukar rayukan ƴan Nijeriya, alhali ba tare da sun aikata wani laifi ba.

Wannan batun, yazo dai dai da yadda a ranar 21 ga watan Yunin 2026, gungugun wasu fusatattun mutane, a kan hanyar  Maraban Jos zuwa garin Zariya a jihar Kaduna, suka yiwa wata Malamar addinin Musulunci Malama Malama Ummulkhair, Usman Aliyu, kisan gilla, ta hanyar ƙone ta da ranta.

Mariganyiyar, mai ƴaƴa biyar, fusatattun mutanen, sun ƙone ta ne, bisa zargin wai, ta saci yara.

ADVERTISEMENT

Wani ƙarin abin baƙin ciki shi ne, kisan gillar ba wai ya auku kai tsaye, a kan titi bane, domin baiwar Allah tuni an miƙa ta a ofishin ƴansanda, kan zargin satar yara, amma duk da haka, gungun marasa imanin suka yiwa ofishin na ƴansandan na Maraban Jos ƙawanya.

An yi zargin cewa, yawan gungun mutanen ne, ya sa suka fi ƙarfin jami’ian ƴansanda da ke a ofishin, wanda hakan ya tilasata su, miƙa matar ga fusatatun mutanen, inda su kuma suka ɗauki doka a hannun su, ta hanyar babbake ta, inda za a iya haka, ya nuna cewa, akwai gazawar samun bayanin sirri.

LABARAI MASU NASABA

Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

Kazalika, aukuwar wannan mummunan yanayi, ya nuna zahirance, na irin sakaci a ɓangaren mahukunta na kare rayuwar waɗanda suke mulka, musamman wanɗada ake tsare da su, a hannun su.

Bayanan da masu gani da ido, a lokacin da lamarin ya auku, musamman kan zargin da aka yiwa DPO ɗin ofishin, na cewa,  shi da kansa ne, ya miƙa matar ga gungun fusatattun muatene da suka yi cirko-cirko a a wajen ofishin, ya nuna irin rashin iya ƙwarewar aiki, na ƴansanda.

Kazalika,  duk da ankararwar da wani ganau a wajen ya yi, na cewa, miƙa matar ga mutanen, zai iya sanya ta rasa ranta, amma DPO ɗin, ya yi ƙememe da shawarar tata.

Haka zalika, ita wata mata a wajen ta yi ƙoƙarin shiga tsakani, amma mutanen suka yi barazar ƙona ta.

Waɗanan zarge-zargen, sun yi hannun Riga da iƙirarin da da DPO ɗin ya yi, na cewa, gungun mutanen sun yi yunƙurin nuna ƙarfin Tuwo, na kaɓar matar da tsiya.

A ɓangaren rundunar ƴansandan jihar ta kawai yi tir da aukuwar lamarin ne, tare da cafko mutane 24 tare da kuma kamo ƙarin wasu, da ake zargi, da aikata wannan  halin na dabbacin tare.

Ya zama wajbi, a gaggauta  gudanar da bincike, zargin rawar da DPO ɗin ya taka da kuma sauran jami’ansa, da ake zargi da hannun kan lamarin, indan an same su da laifi, a hukunta su, kamar yadda dokar ƙasa ta tana.

A ɓangaren mijinta Malam Muhammad Aliyu kuwa, ya bayyana cewa, bayan aukuwar lamarin, ƴaƴansu, sun ci gaba da tambayarasa, shin, ina Mamansu take.

Lamarin ya jefa rayuwar ɗansu mai shekaru 14, a cikin ƙuncin damuwa, tare da yawan furta sai ƙwatowa mahaifiarsu, haƙƙinta.

Ya zama wajibi, rundunar ƴansanda ta ƙasa, ta biya isashiya diyya ga iyalan mariganyiyar.

Gazawar da ƴansanda na rashin kare rauywar waɗanda suke tsare da su a ofis ɗinsu, hakan ne, bai wa ƴan Nijeriya damar, ɗaukar doka a hannun su, inda haka ke ci gaba da zama babar haɗari, musamman kan batun zargin satar yara.

Wannan lamarin zai kuma iya ci gaba da aukuwa, inda a wata rana, zai rkiɗe zuwa dabar siyasa, ko rikicin ƙabilanci, ko kuma addini, da sauran rikice-rikice.

Kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999 da aka sabunta, ya bai wa kowanne ɗan ƙasa, damar yin rayuwa da kare ƴancinsa.

Sai dai, abin baƙin cikin shi ne, Malama Ummulkhairi, ba ta samu wannan kariyar daga gun ƴansanda na kare ranta ba

Ƙungiyoyin addnin Musulunci da dama, kamar irinsu, MULAN, sun yi tir da aukuwar lamarin, tare da yin kira, da a gudanar da cikakken bincike.

Bugu da ƙari, ya zama wajibi, Gwamnatin Kaduna da rundunar ƴansanda ta ƙasa, su ɗauki matakan gaggawa, musamman domin a gudanar da cikakken bincike, tare da tabatar da an hukunta DPO ɗin da wasu jami’ansa, da ake zargi.

Ba za ci gaba da lamuntar yadda wasu ƴan Nijeriya ke ɗaukar doka hannun su ko kuma yiwa dokar karan tsaye, ba tare da wasu ƙwararan hujoji ba, bai kuma kama ace, Jinin Malama Ummulkhairi, ya tafi a banza ba.

Jos
Ra'ayinmu
+ postsBio
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Ce-ce-ku-ce Kan Batun Biyan Bashin Naira Tiriliyan 3.3 Na Kuɗin Lantarki
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Matsalar Ɓacewar Gandun Dazukan Nijeriya

MASU ALAKA

sikila
Ra'ayinmu

Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya

June 26, 2026
Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
Ra'ayinmu

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

May 29, 2026
Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
Labarai

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

May 22, 2026
Next Post
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Shekara 200 Bayan Shehu Ɗan Fodiyo: Hubbarensa Na Ci Gaba Zama Wajen Ziyara Da Neman Tabarruki

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026
Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

July 4, 2026
Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.