ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

by Ra'ayinmu
2 weeks ago

A bisa ƙoƙarin da Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta ƙasa ke ci gaba da yi, na daƙile ci gada da aikata, musamman manyan laifuka, a gidajen da ke a ɗaukacin faɗin ƙasar ne, ta samu nasarar bankaɗowa da kuma lalata, sama da Wayoyin Salula guda 1,167, da wasu masu zaman Jarun, ko dai  suka shiga da su cikin gidan ta ɓarauniyar hanya, ko kuma da haɗin bakin, wasu ma’aikatan a gidajen.

Kazalika, ta kuma bankaɗso ƙarin wasu haramttun kaya, a ɗaukacin gidajen kaso, da ke a ɗaukacin faɗin ƙasar.

Shugaban Hukumar na ƙasa Sylɓester Ndidi Nwakuche, ya ce, an gano tare da kuma ƙwato  kayan ne, a wasu ayyuka da Hukumar ta gudanar, a watanni takwas, da suka gabata, inda ya ce, wasu daga cikinkayan sun haɗa da Wayoyin Salula na alfaram wato smartphones da layukan Waya da katin da ake lodawa Wayoyin da kuma sauran, wasu haramtattun kaya.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, kasancewar waɗannan haramtattun kayan a gidajen gyran hali na ƙasar, lamarin ya zamo, babbar barazana a ɓangaren tsaro, wanda hakan ke bai wa, masu zaman Jarun ɗin damar aikata, manyan laifuka.

Shugaban ya ce, Hukumar ta hukunta jami’an ta, 147, saboda aikata laifuka da ban da ban, na rashin nuna ɗa’a da shigar da haramtattun kaya, zuwa cikin gidajen gyaran hali na ƙasar.

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Bugu da ƙari, Hukumar ta kuma cafke wasu mata biyu, kan zargin su, da  yunƙurin shigar da kayan maye, cikin gidan hali na jihar Kano.

An ruwaito cewa, a watan Afirilun 2026 kacal, akwai sama da masu zaman Jarun 80,000 da ake da su, a  gidajen gidan gyaran hali guda 241 cikinsu, har a sauran wasu cibiyoyin da ake tsare da masu laifi.

Akasarin gidajen a cunkushe suke da masu zaman jarun waɗanda suka kasance, ba a wadata su, da kuɗaɗen gyaransu ba, tare da rashin kula da jin daɗi da walwalar jami’an da ke aiki, a gidajen.

Haka zalika, an ruwaito cewa, a 2025, sama da masu zaman jarun, a wasu gidajen gyaran hali na ƙasar guda 145 suka ranta a na Kare tare da kuma ƙara samun tserwar wasu, daga tsakanin watan Maris zuwa na Agustan 2025.

A hukumance, an kafa gidajen gyaran hali ne, ba wai kaɗai, dolamutaneunta, waɗanda ake tsare da su ba, amma domin gidajen, su kasance, wajen bin doka da oda da kuma sauya nugayen ɗabi’un, waɗanda ake tsare da su.

Amma abin takaicin shi ne, yadda ake ci gaba da samun shigar da Wayuyin Salula da miyagun ƙwayoyi, ta ɓarauniyar hanya, tare da haɗin bakin ɓata garin jami’an da ke kula da gidan, inda hakan ya janyo gidajen, suka koma tamkar bigiren hada-hadar aikata muggan laifuka.

A ra’ayin wannan Jaridar, bankaɗowa da kuma ƙwace miyagun ƙwayoyin tare da kuma ƙwace Wayoyin 1,100, ba wai wani namijin ƙoƙari, Hukumar ta yi ba, kamar yadda ta ke shelanta cewa ta yi, amma kamata ya yi, Hukumar ta fi mayar da hankali, kan lamarin ƙalubalen da gidajen a ɗaukacin faɗin ƙasar, suke ci gaba da fuskanta.

Akuwar waɗannan matsalolin a gidan, hakan ya nuna cewa, har yanzu, akwai sauran Rina a Kaɓa, game da matsakaitan da gidajen ke ciki, duk da iƙirarin samar da sauye-sauyen da Hukumar ke cewa, ta gudanar.

Kazalika, ɗai yi wuya a san shin a tayaya ne, ake shigar da Wayoyin na Salula gidajen, idan har ba ta hanyar haɗa baki da wasu marasa kishin jami’an gidan ba.

A mafi yawancin lokuta, da irin waɗannan Wayoyin ne, ake yin amfani da su, a cikin gidajen, ake tsara yadda za a aikata muggan ayyuka, a cikin alumma kamar irinsu, garkuwa da mutane da fashin a yanar Gizo da fashi da makami.

Bisa waiwayen da wannan Jaridar ta yi, kan rikicin batun zargin da ya.wani fitaccen mai amfani da kafar sada zumunta Martins Otse, da aka fi sani da VeryDarkMan a watan Satumbar  2024 a tsakaninsa da fitaccen Ɗan Daudun nan, Idris Okuneye, da aka fi sani da Bobrisky, inda aka samu ɓullar wata muryar a faifan da aka naɗa, an ji Bobrisky, ya yi zargin cewa, ba a gidsn kason da aka tsare shi, ya kammala zamansa ba.

Bobrisky, a wancan lokacin, ya dage kai da fata cewa, a wani gida na da ban, aka tsare shi ta hanyar sa bakin wasu, masu faɗa aji.

Sai dai, kwamitin bincike, a rahotonsa da ya fitar kan batun ya ce, babu wani ƙamshin gaskiya, kan iƙirarin na Bobrisky, sai kwamtin ya tabbatar da cewa, Bobrisky, ya samu wata alfarma kan batun.

Batun dai, ya haifar da tayar da jijiyar Wuya da zargin cin hanci da rasahawa da cin mutuncin tsarin gidajen gyran hali, da wasu jami’an gidan gyran hali suka kitsa, domin su nuna fifiko, kan batun na Bobrisky.

A zahiri, batun ya wuce maganar ƙwace Wayoyin da kuma miyagun ƙwayoyi, amma babban mahimmancin shi ne, yin komai bisa ƙa’ida da kuma kare ƙimar hukumimim gwamnatin ƙasar.

Koda yake dai, za a iya cewa, Hukumar ya kamata a yaba mata, kan ƙoƙarin hukunta jami’anta, da aka samu hannunsu dumu-dumu, wajen taimaka wa shigar da waɗannan haramtattun kayan cikin gidajen da kuma ƙwace waɗannan kayan.

Haka zalika, abin da ake da matuƙar buƙata shi ne, ci gaba da samar da sauye-sauyen da za a inganta tsarin tare da ci gaba da sanya ido a gidajen.

Haka ya zama wajibi, mahukunta su mayar da hankali wajen ingnata rayuwar jami’an gidan gyran halin, musamman domin a daƙile karɓar na Goro, a tsakaninsu.

Dole ne kuma Gwamnatin Tarayya ta ci gaba da zuba jari a fanin musamman a ɓangaren bayar da horo da sanya na’urorin sanya ido kamar na CCTV, a ɗaukacin gidajen.

Bugu da ƙari, ya zama wajbi, a samar da tsarin kula da lafiyar masu zaman jarun.

Lokaci ya yi da Gwamnatin Tarayya, mai maimakon shelar samar da sauye-sauye a fannin, amma ta tabbatar da dawo da nuna ɗa’a, domin dawo da ƙimar, tsarin.

Matuƙar Gwamnatin ba ta ɗauki wannan matakin ba, tsarin zai ci gaba da zama tamkar ƴar gidan jiya.

Ra'ayinmu
+ postsBio
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Ce-ce-ku-ce Kan Batun Biyan Bashin Naira Tiriliyan 3.3 Na Kuɗin Lantarki
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Matsalar Ɓacewar Gandun Dazukan Nijeriya
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Buƙatar Magance Matsalar Ƙarancin Abinci Mai Gina Jiki A Tsakanin Ƙananan Yara

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Sallar Bana: Yadda Tsadar Ragunan Layya Ke Neman Dusashe Armashinta

Sallar Bana: Yadda Tsadar Ragunan Layya Ke Neman Dusashe Armashinta

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.