ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cika Alkawari Tushe Ne Ga Aiwatar Da Mulki

by CMG Hausa
3 years ago
Cika alkawari

A kan ce “A mai da hankali kan aikace-aikacen wani, maimakon maganarsa”. Yayin da ake tantance aikin gwamnati ma, haka abun yake. Idan wata gwamnati ta iya cika alkawarin da ta dauka, to, jama’a za su amince da ita, sa’an nan za a samu damar gudanar da harkokin mulki yadda ake bukata.

A yau lahadi, firaministan kasar Sin Li Keqiang, ya gabatar da rahoton ayyukan gwamnati a gun taron shekara-shekara na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin. Idan an kwatanta rahoto na wannan shekara, da na bara, za a fahimci yadda gwamnatin kasar ta yi kokarin cika alkawari a shekarar 2022.

  • An Gudanar Da Bikin Murnar Cika Shekaru 40 Da Kulla Huldar Diplomassiya Tsakanin Sin Da Cote d’Ivoire

In mun duba fannin samar da guraben aikin yi, gwamnatin kasar Sin ta yi shirin samar da guraben aikin yi ga karin mutane fiye da miliyan 11 a shekarar 2022, daga baya a hakika ta samar da guraben aikin yi miliyan 12 da dubu 60. A fannin farashin kayayyaki, kasar ta yi shirin kayyade karuwar farashin kayayyaki cikin kashi 3%. Daga bisani ta samu karuwar da ba ta wuce kashi 2% ba. Sa’an nan a fannin samar da hatsi, da ma gwamnatin kasar ta yi shirin samar da hatsin da yawansa ya wuce kilo biliyan 650, inda adadi na hakika da ta samu ya kai kimanin kilo biliyan 686.6.

ADVERTISEMENT

Wadannan jimiloli sun nuna cewa gwamnatin kasar Sin ta cimma burikan da ta sanya a fannoni daban daban. Ban da jimilar GDP, wadda ta yi shirin samun karuwarta ta kashi 5.5%, amma hakikanin karin da ta samu ya kasance kashi 3%. Sai dai wannan batu ba wani abu mai wuyar fahimta ba ne, saboda annobar cutar COVID-19, da yakin da ake yi tsakanin Ukraine da Rasha, da yadda kasar Amurka ta sa ruwan kudin ajiya a bankunanta ya karu, wadanda duka suka haifar da matsala ga tattalin arzikin duniya. Ta yin la’akari da wannan yanayin da ake ciki, karuwar da tattalin arzikin Sin ya samu ba wani abu mai sauki ba ne, kana tana kan gaba a duniya wajen kiyaye karuwar tattalin arziki.

Rahoton da Li ya gabatar, ya kuma shafi yadda kasar Sin ta yi kokarin zamanintar da kai cikin shekaru 5 da suka wuce, inda ta daidaita matsalar talauci daga tushenta, da kare wata matsakaiciyar karuwar GDP ta kashi 5.2%, da samun karuwar bangaren masana’antu mai alaka da fasahohin zamani da ta kai kashi 10.6%, da sanya tsawon layin dogon jirgin kasa mai saurin gudu karuwa daga kilomita dubu 25 zuwa kilomita dubu 42, da dai sauransu. Ta yin la’akari da wadannan nasarorin da aka samu, ba za a yi mamaki ba ganin burin raya kasa da gwamnatin kasar Sin ta gabatar ma majalisar wakilan jama’ar kasar a matsayin shawara, wanda ya hada da neman samun karuwar GDP kimanin kashi 5%, da samar da sabbin guraben aikin yi ga karin mutane miliyan 12, da dai makamantansu. Domin wannan buri bai wuce matsakaiciyar karuwar da tattalin arzikin Sin ya samu cikin shekaru 5 da suka wuce ba.

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Cikin shekarar 2022 da ta gabata, na taba gamuwa da mutane da yawa, wadanda annobar COVID-19 ta yi tasiri kan zaman rayuwarsu, a birnin Beijing. Cikinsu akwai mai kantin sayar da kofi, wanda harkar kantinsa ta gamu da matsala, da mai jigilar kaya, wanda ya ci gaba da aiki har zuwa tsakar dare, da mai yi wa mutane masu yawon shakatawa jagora, wanda ya fara wani aiki na daban na wucin gadi. Sai dai na ga akwai wasu abubuwa na bai daya a cikin zukatansu, wato hakuri da fara’a: Sun yarda cewa duk wata matsala, za a ga bayanta, kana nan gaba za a samu makoma mai haske. To me ya sa suke da wannan imani? Saboda sun dade suna shaidawa da idanunsu, yadda kasarsu ta samu nasarar daidaita matsaloli daban daban, da cika dukkan alkawuran da ta yi.

Sai wata gwamnati ta cika alkawarinta, sannan jama’a za su amince da ita, sa’an nan muddin jama’a sun yarda da gwamnati, to, za a samu damar aiwatar da matakan raya kasa yadda ake bukata. Saboda haka, ana iya ce, cika alkawari tushe ne ga aiwatar da mulki ta wata nagartacciyar hanya. (Bello Wang)

Cika alkawari
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji
Daga Birnin Sin

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina
Daga Birnin Sin

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Next Post
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa 2 Da Ceto Mutum 1 A Bauchi

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa 2 Da Ceto Mutum 1 A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.