ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CMG Za Ta Nunawa Duniya Yadda Ake Hadin Gwiwar Moriyar Juna

by CGTN Hausa
3 years ago
CMG

Gabanin babban taron kasa da kasa dangane da hadin gwiwa bisa shawarar Ziri Daya da Hanya Daya dake cika shekaru 10 a bana, babban rukunin gidajen talabijin da rediyo na kasar Sin CMG, ya kaddamar da hadin gwiwa da kafofin watsa labarai na kasashen dake aiwatar da shawarar.

Hakika waka a bakin mai ita ta fi dadi. Wannan hadin gwiwa zai bada damar bayar da cikakku kuma sahihan labaran kasar Sin da ainihin yanayin da ake ciki dangane da shawarar kamar yadda ya kamata, ga al’ummomin duniya. Haka kuma, zai taka rawa wajen wayar da kan kasashen duniya game da irin alfanun shawarar da ayyukan da ake aiwatarwa a karkashinta.

  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Jadda ‘Yancin Dan Adam Wajen Samun Kiwon Lafiyar Kwakwalwa
  • Sin Ta Yi Allah Wadai Da Harin Jirage Marasa Matuka Da Aka Kai Kan Wata Makarantar Soji A Syria

A ganina, kasar Sin ba ta samu yabon da ya kamata game da ayyuka da tallafi da shawarwari da ma dabarun samar da ci gaba da zaman lafiya da take gabatarwa a duniya, saboda yadda wasu kasashe suka dukufa wajen shafa mata bakin fenti. A yanzu, kasar Sin da ta jagoranci gabatar da shawarar tare da raya ta, za ta samu damar bayar da labari da bakinta ta hannun CMG, yayin da kafofin watsa labarai na kasashen da shawarar ta shafa, za su watsa wadannan sahihan labarai da bayanai ga al’ummominsu, lamarin da zai sa jama’ar kasa da kasa su kyautata fahimtarsu kan kasar Sin.

ADVERTISEMENT

Kasancewar kafofin yada labarai, matsayin masu ilmantarwa da wayar da kan al’umma, wannan hadin gwiwa zai taimaka gaya wajen kore jita-jita da dukkan wasu labarai na karya da ake yadawa. Ta hakan ne kuma, al’ummomin duniya za su gane matsayin kasar Sin na mai neman daidaito da moriyar juna tsakanin kasa da kasa dake da burin gina al’umma mai makoma ta bai daya.

Da yake gabatar da jawabi, shugaban CMG Shen Haixiong, ya ce CMG ta sa hannu kan yarjejeniyoyin watsa labaru da kafofin yada labaru 682 daga kasashe 15 domin yada shirye-shirye gane da shawarar. Wannan gagarumin ci gaba ne la’akari da cewa, cikar shawarar shekaru goma ta nuna cewa tana kara bunkasa, don haka akwai bukatar kara wayar da kai game da burika da manufofin kasar Sin na hadin gwiwa, domin al’ummun duniya su gane cewa, yanzu an shiga wani babi na hadin gwiwar moriyar juna bisa adalci da daidaito, maimakon wanda aka saba gani na cin nasara daga faduwar wani bangare.

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Ko shakka babu, ina da yakinin bisa irin jajircewarta, CMG za ta cimma burinta, kuma duniya za ta fahimci ainihin kasar Sin.

CMG
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

MASU ALAKA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
Daga Birnin Sin

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Daga Birnin Sin

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Next Post
Gwamnatin Kasar Sin Ta Amince Da Takardun Ba Da Tabbacin Zaman Al’umma Da ’Yancin Mallakar Fasaha

Gwamnatin Kasar Sin Ta Amince Da Takardun Ba Da Tabbacin Zaman Al'umma Da ’Yancin Mallakar Fasaha

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.