ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CMG Za Ta Nunawa Duniya Yadda Ake Hadin Gwiwar Moriyar Juna

by CGTN Hausa
3 years ago
CMG

Gabanin babban taron kasa da kasa dangane da hadin gwiwa bisa shawarar Ziri Daya da Hanya Daya dake cika shekaru 10 a bana, babban rukunin gidajen talabijin da rediyo na kasar Sin CMG, ya kaddamar da hadin gwiwa da kafofin watsa labarai na kasashen dake aiwatar da shawarar.

Hakika waka a bakin mai ita ta fi dadi. Wannan hadin gwiwa zai bada damar bayar da cikakku kuma sahihan labaran kasar Sin da ainihin yanayin da ake ciki dangane da shawarar kamar yadda ya kamata, ga al’ummomin duniya. Haka kuma, zai taka rawa wajen wayar da kan kasashen duniya game da irin alfanun shawarar da ayyukan da ake aiwatarwa a karkashinta.

  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Jadda ‘Yancin Dan Adam Wajen Samun Kiwon Lafiyar Kwakwalwa
  • Sin Ta Yi Allah Wadai Da Harin Jirage Marasa Matuka Da Aka Kai Kan Wata Makarantar Soji A Syria

A ganina, kasar Sin ba ta samu yabon da ya kamata game da ayyuka da tallafi da shawarwari da ma dabarun samar da ci gaba da zaman lafiya da take gabatarwa a duniya, saboda yadda wasu kasashe suka dukufa wajen shafa mata bakin fenti. A yanzu, kasar Sin da ta jagoranci gabatar da shawarar tare da raya ta, za ta samu damar bayar da labari da bakinta ta hannun CMG, yayin da kafofin watsa labarai na kasashen da shawarar ta shafa, za su watsa wadannan sahihan labarai da bayanai ga al’ummominsu, lamarin da zai sa jama’ar kasa da kasa su kyautata fahimtarsu kan kasar Sin.

ADVERTISEMENT

Kasancewar kafofin yada labarai, matsayin masu ilmantarwa da wayar da kan al’umma, wannan hadin gwiwa zai taimaka gaya wajen kore jita-jita da dukkan wasu labarai na karya da ake yadawa. Ta hakan ne kuma, al’ummomin duniya za su gane matsayin kasar Sin na mai neman daidaito da moriyar juna tsakanin kasa da kasa dake da burin gina al’umma mai makoma ta bai daya.

Da yake gabatar da jawabi, shugaban CMG Shen Haixiong, ya ce CMG ta sa hannu kan yarjejeniyoyin watsa labaru da kafofin yada labaru 682 daga kasashe 15 domin yada shirye-shirye gane da shawarar. Wannan gagarumin ci gaba ne la’akari da cewa, cikar shawarar shekaru goma ta nuna cewa tana kara bunkasa, don haka akwai bukatar kara wayar da kai game da burika da manufofin kasar Sin na hadin gwiwa, domin al’ummun duniya su gane cewa, yanzu an shiga wani babi na hadin gwiwar moriyar juna bisa adalci da daidaito, maimakon wanda aka saba gani na cin nasara daga faduwar wani bangare.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Ko shakka babu, ina da yakinin bisa irin jajircewarta, CMG za ta cimma burinta, kuma duniya za ta fahimci ainihin kasar Sin.

CMG
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
Daga Birnin Sin

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Next Post
Gwamnatin Kasar Sin Ta Amince Da Takardun Ba Da Tabbacin Zaman Al’umma Da ’Yancin Mallakar Fasaha

Gwamnatin Kasar Sin Ta Amince Da Takardun Ba Da Tabbacin Zaman Al'umma Da ’Yancin Mallakar Fasaha

LABARAI MASU NASABA

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.