ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 29, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Gaske Ne Babu Tashar Samar Da Lantarki Ta Karfin Iska A Kasar Sin?

by Sulaiman and CGTN Hausa
5 months ago
Lantarki

A gun taron dandalin tattaunawa kan tattalin arzikin duniya na shekarar 2026 da aka gudanar kwanan nan ba da jimawa ba a birnin Davos na kasar Switzerland, shugaban kasar Amurka Donald Trump ya sake firgita duniya bisa kalamansa na wai “Kasar Sin ta kera dimbin injunan samar da lantarki ta karfin iska, amma ban taba ganin tashar samar da lantarki ta karfin iska ko daya a kasar Sin ba”.

 

Amma ko haka lamarin yake?

ADVERTISEMENT

Masu karatu, idan kun samu damar zuwa kasar Sin, lallai kam akasin hakan za ku gani, duba da cewa, daga teku zuwa hamada, daga tuddai zuwa filaye, jerin injunan samar da lantarki ta karfin iska ne za ku gani a tsaye, wadanda suke juya karfin iska zuwa wutar lantarki tare da samar da su ga magidanta mabambanta. A lardin Gansu da ke arewa maso yammacin kasar, cibiyar samar da lantarki ta karfin iska ta Jiuquan na iya samar da lantarki da yawansa ya wuce KW miliyan 10, wanda har ma ake iya hango ta daga sararin samaniya sakamakon girmanta. Amma me ya hana shugaba Trump iya ganinta?

 

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Ko kafofin yada labarai na kasashen yamma ma sun kasa hakuri da furucin shugaba Trump maras tushe, inda jaridar The Guardian ta kasar Burtaniya ta yi nuni da cewa, abin da ya furta ba gaskiya ba ne. A rahoton da jaridar ta wallafa, ta jaddada cewa, kasar Sin ita ce ta farko a duniya wajen iya samar da wutar lantarki ta karfin iska, har ma yawan lantarkin da take iya samarwa ta yin amfani da tashoshin samar da lantarki ta karfin iska da take ginawa ya ninka na sauran kasashen duniya baki daya sau biyu. Har ila yau, mujallar Time ta kasar Amurka ta ruwaito rahoton kwamitin kula da makamashin iska na duniya na GWEC yana cewa, a shekarar 2024, sabbin injunan samar da lantarki ta karfin iska da kasar Sin ta kafa sun dau kaso 70% na duniya baki daya, wadanda ke iya samar da lantarki da yawansa ya zarce GW 520, wato kusan rabi na duniya baki daya ke nan. Akwai kuma mai bibbiyar shafukan sada zumunta da ya bayyana cewa, “wani abokina ya dawo daga yawon shakatawa a kasar Sin, kuma ya gani da idonsa injunan samar da lantarki ta karfin iska da aka kafa kusan ko ina a kasar.”

 

Alal hakika, a cikin shekaru 10 da suka wuce, ayyukan samar da lantarki ta karfin iska sun bunkasa cikin sauri a kasar Sin, har ma kasar ta shiga sahun gaba a duniya. Ya zuwa karshen watan Nuwamban bara, yawan lantarki da kasar Sin ke iya samarwa ta karfin iska ya zarce KW miliyan 600, inda kasar ta kiyaye matsayinta na farko a duniya a fannin karfinta na wannan bangare tsawon shekaru 15 a jere. Sai dai adadin ba kawai ya bayyana saurin bunkasar kasar ta fannin yin amfani da karfin iska wajen samar da lantarki ba ne, har ma ya shaida irin sauye-sauyen da ke faruwa ga salon bunkasar kasar.

 

Hasali ma dai, baya ga kasancewarta kasa ta farko wajen samar da lantarki ta karfin iska a duniya, kasar Sin ta kuma kasance ta farko wajen samar da lantarki ta makamashin rana, kuma tana sahun gaba a duniya ta fannin samar da lantarki ta karfin ruwa. Hakan ya faru ne sakamakon irin fasahohin ci gaba da ma cikakken tsarin masana’antu masu alaka da sabbin makamashi da kasar ke da su a duniya, kuma ainihin abin da ya haifar da hakan shi ne manufar kasar Sin ta tabbatar da bunkasa ba tare da gurbata muhalli ba. Cimma burin kaiwa kololuwar fitar da hayakin Carbon zuwa shekarar 2030, da kuma kawar da illarsa zuwa shekarar 2060, ba kawai ya kasance alkawarin da kasar Sin ta dauka a gaban kasa da kasa ba ne, hatta ma wani abu ne da ita kanta take bukata wajen inganta ci gabanta.

 

A jawabin da ya gabatar a taron Davos, shugaba Trump ya ce, kullum kasar Sin na sayar da injunan samar da lantarki ta karfin iska ga “masu shirme”. Sai dai hakikanin abin da ya faru shi ne, kasar Sin na kokarin hadin gwiwa da sauran kasashe wajen tabbatar da bunkasa ba tare da gurbata muhalli ba, inda ta raba gajiyar nasarorin da ta cimma ta fannin rage fitar da hayakin Carbon ga kasa da kasa. A cikin ’yan shekarun baya, kasar Sin ta fitar da kayayyakinta masu alaka da samar da lantarki ta karfin iska da ta hasken rana da ma motocin lantarki zuwa kasashe da shiyyoyi sama da 200 a fadin duniya. Alkaluman da aka samar sun shaida cewa, daga shekarar 2021 zuwa ta 2025, kayayyaki masu alaka da samar da lantarki ta karfin iska da ta hasken rana da kasar Sin ta fitar zuwa ketare sun taimaka ga rage fitar da hayakin Carbon kimanin tan biliyan 4.1 a kasashen. A sa’i daya kuma, sakamakon cikakken tsarin masana’antun samar da kayayyakin da ma fasahohinta masu ci gaba, kudin da kasa da kasa suka biya wajen samar da lantarki ta karfin iska da makamashin rana sun ragu da kaso 60% da 80% kowanensu. A nahiyar Afirka, kasar Sin ta aiwatar da hadin gwiwa da sama da rabin kasashen nahiyar ta fannin samar da sabbin makamashi, wanda hakan ya inganta harsashin kasashen wajen raya masana’antu da kuma zamanantar da kansu. To, maganar wayo ko shirme, tana kan wanda ya ga hakan ne.

 

Daga karshe, muna maraba da shugaba Trump da ya kawo ziyarar gani da ido tashoshin samar da lantarki ta karfin iska a kasar Sin, kuma tabbas injunan samar da lantarki ta karfin iska da aka kafa a sassa daban daban na kasar Sin za su ba shi amsa.

Lantarki
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao
  • Sulaiman
    Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu
  • Sulaiman
    Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna
Lantarki
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Da Gaske Ne Babu Tashar Samar Da Lantarki Ta Karfin Iska A Kasar Sin?

Da Gaske Ne Babu Tashar Samar Da Lantarki Ta Karfin Iska A Kasar Sin?

LABARAI MASU NASABA

Hatsarin Mota Ya Kashe Dalibin FUDMA, Wasu 17 Sun Jikkata A Katsina

Hatsarin Mota Ya Kashe Dalibin FUDMA, Wasu 17 Sun Jikkata A Katsina

June 29, 2026
Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao

Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao

June 28, 2026
Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

June 28, 2026
An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

June 28, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

June 28, 2026
Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

June 28, 2026
Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

June 28, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.