ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Karyata Maganar Wai Akwai “Matsin Kasar Sin”

by Sulaiman and Bello Wang
3 hours ago
Sin

Tsohon sakataren harkokin wajen kasar Amurka, Mike Pompeo, ya taba bayyana salon Amurka na tsoma baki a harkokin duniya da cewa, “Muna yin karya, muna yaudara, muna kuma sata.” Ya ce, “Hakan ya nuna halayyar kasar Amurka mai alfahari yayin neman ci gaba.” Bari mu tuna da wannan magana, domin da gaske ita ce ka’idar da kasar Amurka take bi, yayin da take gabatar da maganganu da aiwatar da ayyuka daban daban.

A kwanan baya, wata cibiyar nazari ta kasar Amurka, wato “Peterson Institute for International Economics” ta fitar da wani rahoto mai kunshe da sabon ra’ayi na wai “matsin kasar Sin”, wai masana’antun kasar Sin ba ma kawai suna haifar da matsin lamba ga bangaren hada kayayyaki na Turai da Amurka ba, har ma suna matsawa masana’antun sauran kasashe masu tasowa. Wannan sabon ra’ayi, an kirkiro shi ne bisa tushen laifin da kasashen yamma suka dora wa kasar Sin wai kasar na “samar da kayayyaki fiye da kima”, sai dai ra’ayin da aka gabatar a wannan karo ya nuna niyyar haifar da rashin jituwa tsakanin kasashe masu tasowa.

Amma, yadda Amurka ke kokarin shafa wa kasar Sin bakin fenti wani abu ne da har Amurkawa da kansu ba za su yarda da shi ba. Misali, Lawrence Freeman, wani mai sharhi kan harkokin siyasa da tattalin arziki dan kasar Amurka, wanda ya kware a fannin nazarin manufofin tattalin arzikin kasashen Afirka, ya rubuta wani bayani a kwanan nan, inda ya bayyana cewa mutanen da suka kirkiro ra’ayin “matsin kasar Sin” sam ba su da gaskiya.

ADVERTISEMENT

Lawrence Freeman ya ce, bisa ra’ayin “matsin kasar Sin”, ana ikirarin cewa “rarar cinikayyar kasar Sin tana gurtunta masana’antun kasar Amurka”. Sai dai maganar ba ta da tushe. A cewar Freeman, Amurka ta fara durkusa bangarenta na hada kayayyaki da kanta tun a farkon shekarun 1980. A wancan lokacin, Amurka ta nemi kafa wata al’umma maras dogaro kan masana’antu a cikin gidanta, inda ta fara rufe galibin masana’antu, ban da masu hada makamai da sauran kayayyaki masu kunshe da fasahohin zamani. Ban da haka, kasar ta zama cibiyar hada-hadar kudi, gami da kokarin raya bangaren samar da hidimomi.

Yayin da a nata bangare, kasar Sin ba ta samu cikakken karfi a fannin masana’antu ba a lokacin.Dangane da ikirarin cewa wai “kasar Sin tana tare hanyar sauran kasashe masu tasowa a fannin raya masana’antu”, mista Freeman ya dauki nahiyar Afirka a matsayin misali, yana mai cewa, alal hakika kasar Amurka da sauran kasashen yamma ne ke da alhakin haddasa koma baya a kasashen Afirka ta fuskar masana’antu. A cewarsa, tun daga shekarun 1940 har zuwa lokacin da kasar Sin ta fara zama kasa mai karfin tattalin arziki a shekarar 2000, tsarin tattalin arzikin duniya ya dade yana karkashin jagorancin kasar Amurka da sauran kasashen dake yammacin duniya. Su ne, maimakon kasar Sin, ke da alhakin gaza tabbatar da ci gaban tattalin arziki a dimbin kasashe masu rauni, cikin tsawon shekaru 60.

LABARAI MASU NASABA

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?

Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

Dalilin da ya sa haka, a cewar mista Freeman, shi ne “manufofin kasashen yamma ba su taba kunsar niyyar shigar da kasashen Afirka cikin tsarin samar da kayayyaki na duniya ba.” Akasin haka, kasar Sin, ta hanyar aiwatar da shawarar Ziri Daya da Hanya Daya (BRI), ta gina dimbin ababen more rayuwa a kasashe daban daban, wadanda suka kasance tushen bunkasa masana’antu.

Mista Freeman ya kara da cewa, “Da babu shawarar BRI, da yanayin rayuwar yawancin mutanen kasashen Afirka ya fi muni.”Za a iya daukar sabon ra’ayin da bangaren Amurka ya kirkira a wannan karo a matsayin wani matakin da ya bayyana niyyar kasar ta hana kasar Sin samun ci gaba. Sai dai duk wata maganar da kasar Amurka za ta fada, ba za ta karkata hankalinmu daga tunawa da zancen mista Mike Pompeo da ya shafi “halayyar kasar Amurka mai alfahari” ba. (Bello Wang)

Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Ta Fitar Da Takardar Matsayinta Kan Shugabancin Intanet A Zamanin Fasahohin Zamani
  • Sulaiman
    Shugaba Xi Ya Jaddada Muhimmancin Gina Halaye Nagari Ta Hanyar Ilimi Da Inganta Tsarin Ilimi Na Tushe A Matakin Koli
  • Sulaiman
    Rajistar Shirin Auren Gata Na Kano Kyauta Ce, In Ji Hukumar Hisbah
  • Sulaiman
    Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa
Sin
Bello Wang
+ posts Bio
  • Bello Wang
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-wang/
    Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Dama Ce Ga Kasashen Afirka

MASU ALAKA

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?
Ra'ayi Riga

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?

July 20, 2026
Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI
Ra'ayi Riga

Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

July 19, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Ra'ayi Riga

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Next Post
Hisbah

Rajistar Shirin Auren Gata Na Kano Kyauta Ce, In Ji Hukumar Hisbah

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Fitar Da Takardar Matsayinta Kan Shugabancin Intanet A Zamanin Fasahohin Zamani

Sin Ta Fitar Da Takardar Matsayinta Kan Shugabancin Intanet A Zamanin Fasahohin Zamani

July 22, 2026
Shugaba Xi Ya Jaddada Muhimmancin Gina Halaye Nagari Ta Hanyar Ilimi Da Inganta Tsarin Ilimi Na Tushe A Matakin Koli

Shugaba Xi Ya Jaddada Muhimmancin Gina Halaye Nagari Ta Hanyar Ilimi Da Inganta Tsarin Ilimi Na Tushe A Matakin Koli

July 22, 2026
Hisbah

Rajistar Shirin Auren Gata Na Kano Kyauta Ce, In Ji Hukumar Hisbah

July 22, 2026
An Karyata Maganar Wai Akwai “Matsin Kasar Sin”

An Karyata Maganar Wai Akwai “Matsin Kasar Sin”

July 22, 2026
Sojoji Sun Daƙile ‘Yan Ta’adda Daga Karɓar Haraji A Yobe

Sojoji Sun Daƙile ‘Yan Ta’adda Daga Karɓar Haraji A Yobe

July 22, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara, Katsina Da Kebbi

July 22, 2026
NNPP Ta Yi Barazanar Maka INEC A Kotu Kan Ƙin Bin Umarnin Dawo Da Tambarinta A Kan Lokaci

NNPP Ta Yi Barazanar Maka INEC A Kotu Kan Ƙin Bin Umarnin Dawo Da Tambarinta A Kan Lokaci

July 22, 2026
Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

July 22, 2026
Shugaban Laliga Ya Buƙaci Infantino Ya Sauka Daga Shugabancin FIFA

Shugaban Laliga Ya Buƙaci Infantino Ya Sauka Daga Shugabancin FIFA

July 22, 2026
Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

July 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.