Wani rahoto da kungiyar masana’antar manhajoji ta kasar Sin ta fitar a ranar Litinin ya nuna cewa, a yayin shirin raya tattalin arziki da zamantakewar al’umma na kasar Sin na shekaru biyar-biyar karo na 15 da za a aiwatar tsakanin shekarar 2026 zuwa 2030, ana hasashen girman masana’antar manhajoji ta kasar Sin zai wuce Yuan tiriliyan 20, kimanin dala tiriliyan 2.9.
Rahoton bincike na “Hasashen Ci Gaban Masana’antar Manhajoji ta Kasar Sin na 2025” ya nuna cewa, a watanni biyun farko na wannan shekara, kudaden shiga na ayyukan manhajoji ya kai Yuan tiriliyan 2.15, wanda ya karu da kashi 11.7% idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata. Kazalika, jimillar ribar masana’antar ta kai Yuan biliyan 269.3, wanda ya karu da kashi 7.3%.
Rahoton ya ce, masana’antar ta taka muhimmiyar rawa wajen saita karkacewar hanyar da masana’antu ke bi, zuwa zamani na dijital da kuma na hikima.Mataimakin ministan masana’antu da fasahar sadarwa Xiong Jijun ya bayyana cewa, kasar Sin za ta ciyar da aiwatar da tsarin aiki na musamman na “AI+Manhajoji” gaba, don karfafa matakin da masana’antar ke dauka na saita hanyarta zuwa zamani na hikima, da kuma inganta, da kyautata samfuran manhajoji, da yiwa kamfanoni masu ruwa da tsaki kwaskwarima ta hanyar fasaha da kimiya, tare da tallafa wa sabbin nau’ikan tsarin sarrafawa mai amfani da fasahar AI, da sabbin manhajojin masana’antu na hikima da dai sauran sabbin nau’inka. (Amina Xu)















Discussion about this post