A yau Laraba ne aka gudanar da taron matakin koli karo na uku na dandalin aikin raba ci gaban duniya a nan birnin Beijing. Darektan ofishin harkokin waje na kwamitin tsakiyar JKS Wang Yi ya halarci bikin bude taro kuma ya yi jawabi.
Cikin jawabi nasa, Wang Yi ya ce bana ita ce shekara ta 5 tun bayan da shugaba Xi Jinping ya gabatar da “shawarar ci gaban duniya”. A cikin shekaru 5 da suka wuce, bisa kokarin bangarori daban-daban, “shawarar ci gaban duniya” ta fadada daga shawarar Sin zuwa yarjejeniya ta kasa da kasa.
Bangaren Sin zai dauki matakai masu kyau, da zurfafa hadin gwiwa, kuma zai ci gaba da zama mai hanzari da bayar da gudunmawa ga ci gaban duniya.
Hukumar ingiza ci gaban kasa da kasa ta hadin gwiwa ta kasar Sin ce ta shirya wannan taro. Kuma shugabannin kasashen Mozambique da Ghana, da sauran shugabannin kasashe, da kuma mataimakiyar babban sakataren MDD Amina Mohammed da wakilai, sun halarci taron ko gabatar da jawabi ta bidiyo.
Bugu da kari, wakilai daga kasashe, da kungiyoyin kasa da kasa, da sauran cibiyoyi sama da 140, sun halarci taron ta kafar bidiyo wasu kuma a zahiri. (Amina Xu)














Discussion about this post