ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, September 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Diflomasiyyar Sin Ta Ciri Tuta!

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
Sin

’Yan kwanaki bayan shiga sabuwar shekarar nan ta 2026, duniya na ci gaba da fuskantar yanayi na tangal-tangal, kana muna ta jin labarai marasa dadi na tashe-tashen hankula a wasu sassan duniya daban daban. To sai dai kuma duk da haka, a daya bangaren, muna iya cewa mun shiga sabuwar shekarar ta bana da kyakkyawan fatan kyautatuwar lamura, musamman ganin yadda salon diflomasiyyar kasar Sin ke kara samar da tagomashi ga cundayar al’ummun duniya bisa mutunta juna, da yunkurin kare moriyar juna, da adawa da matakan kashin kai, ko keta hurumin ’yancin kasashe na mulkin kai da kiyaye yankunansu.

Mun ga yadda manyan jami’an Sin suka bude shekarar da ziyartar kasashen ketare da dama, domin sada zumunta, da kara yaukaka fahimtar juna, ciki har da ziyarar da ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya kai kasashen Habasha, da Tanzania da Lesotho dake nahiyar Afirka. Ziyarar da ta kasance karo na 36 a jere da ministan wajen kasar Sin ke zuwa kasashen Afirka a duk farkon shekara. Ta kuma zo a gabar da ake cika shekaru 70 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da kasashen Afirka.

Masharhanta na cewa, wannan ziyara ta alamta yadda kasar Sin ta dukufa wajen zurfafa kawance bisa adalci, da daidaito, da martaba juna, da burin cimma moriya tare. Ta hanyar aiwatar da matakai na zahiri, kasar Sin ta ci gaba da ingiza daidaito, da karsashi ga ci gaban duniya duk da tarin kalubale da ake fama da su.

ADVERTISEMENT

A kurkusa ma, kasar Sin na kara kyautata cudanya, da zumunci tare da makwaftanta, kamar dai yadda muka ga kokarin kasar na zurfafa tattaunawa da kasashe irin su Pakistan, da Koriya ta kudu, da nufin haifar da karin daidaiton alakar makwaftaka, da aminci da bunkasa hadin gwiwa.

Har ila yau, yayin da kasashe da dama ke shan radadin karin harajin fito daga matakan kasar Amurka, a nata bangare kasar Sin ta bullo da manufar janye daukacin harajin kwastam kan hajojin dake shiga kasar daga kasashen Afirka dake da huldar diflomasiyya tare da ita, wanda hakan ke kara shaida kwazon kasar Sin na tallafawa, da goyon bayan muradun kasashe masu tasowa na samun ci gaba cikin lumana.

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi

Ministan Kimiyya Na Afirka Ta Kudu Ya Yi Kiran Zurfafa Hadin Gwiwar Kimiyya Da Fasaha Da Sin

Yayin da ake ganin yunkurin wasu manyan kasashen duniya na kafa tsarin danniya da babakere, da kulla kawancen mayar da wasu sassa saniyar ware, a nata bangare kuwa, kasar Sin ta dukufa ne wajen shawo kan kalubalolinta na cikin gida, da kuma raba damammakin ci gabanta mai inganci ga sauran sassan kasa da kasa, karkashin salon diflomasiyyar ta dake cike da fatan cimma nasara cikin lumana, da gina al’ummar duniya mai makomar bai daya ga dukkanin bil’adama. Salon diflomasiyyar da ke shan jinjinawa da goyon baya daga dukkanin kasashe masu fatan a “gudu tare a tsira tare”!(Saminu Alhassan)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Samu Babban Sakamako Kan Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa Na Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ministan Kimiyya Na Afirka Ta Kudu Ya Yi Kiran Zurfafa Hadin Gwiwar Kimiyya Da Fasaha Da Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Ya Gabatar Da Shawarwari Kan Hadin Gwiwar “Gawurtacciyar Kungiyar BRICS”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ya Kamata A Rike Damar Kasar Sin Samfurin 2.0 A Taron CIFIT
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi
  • Sulaiman
    An Samu Babban Sakamako Kan Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa Na Duniya
  • Sulaiman
    Ministan Kimiyya Na Afirka Ta Kudu Ya Yi Kiran Zurfafa Hadin Gwiwar Kimiyya Da Fasaha Da Sin
  • Sulaiman
    Gwamna Uba Sani Ya Amince Da Ƙarin Albashi Ga Ma’aikatan KASU

MASU ALAKA

Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi
Daga Birnin Sin

Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi

September 13, 2026
Ministan Kimiyya Na Afirka Ta Kudu Ya Yi Kiran Zurfafa Hadin Gwiwar Kimiyya Da Fasaha Da Sin
Daga Birnin Sin

Ministan Kimiyya Na Afirka Ta Kudu Ya Yi Kiran Zurfafa Hadin Gwiwar Kimiyya Da Fasaha Da Sin

September 13, 2026
Xi Ya Gabatar Da Shawarwari Kan Hadin Gwiwar “Gawurtacciyar Kungiyar BRICS”
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gabatar Da Shawarwari Kan Hadin Gwiwar “Gawurtacciyar Kungiyar BRICS”

September 13, 2026
Next Post
EFCC Ta Gabatar Da Ƙarin Hujjoji A Shari’ar Tsohon Gwamnan Kogi, Yahaya Bello

EFCC Ta Gabatar Da Ƙarin Hujjoji A Shari’ar Tsohon Gwamnan Kogi, Yahaya Bello

LABARAI MASU NASABA

Manchester Derby: City Ta Nunawa United Kwanji A Old Trafford

Manchester Derby: City Ta Nunawa United Kwanji A Old Trafford

September 13, 2026
Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

September 13, 2026
Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

Makiyaya Sun Yi Asarar Shanu 200,000 Ta Dalilin Rikice-Rikice – MACBAN

September 13, 2026
Sin

Farashin Man Fetur Ya Sake Tashi A Abuja

September 13, 2026
Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi

Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi

September 13, 2026
Sin

Malamai Da Limamai 3,000 Sun Yi Addu’ar Zaman Lafiya Da Nasarar Tinubu A 2027

September 13, 2026
An Samu Babban Sakamako Kan Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa Na Duniya

An Samu Babban Sakamako Kan Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa Na Duniya

September 13, 2026
Ministan Kimiyya Na Afirka Ta Kudu Ya Yi Kiran Zurfafa Hadin Gwiwar Kimiyya Da Fasaha Da Sin

Ministan Kimiyya Na Afirka Ta Kudu Ya Yi Kiran Zurfafa Hadin Gwiwar Kimiyya Da Fasaha Da Sin

September 13, 2026
Sin

An Gudanar Da Sallar Zana’idar Tsohon Gwamnan Gongola

September 13, 2026
Yajin Aikin ASUU: Malaman Jami’ar Jihar Kaduna Sun Bijirewa El-rufa’i

Gwamna Uba Sani Ya Amince Da Ƙarin Albashi Ga Ma’aikatan KASU

September 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.