ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Diflomasiyyar Sin Ta Ciri Tuta!

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
Sin

’Yan kwanaki bayan shiga sabuwar shekarar nan ta 2026, duniya na ci gaba da fuskantar yanayi na tangal-tangal, kana muna ta jin labarai marasa dadi na tashe-tashen hankula a wasu sassan duniya daban daban. To sai dai kuma duk da haka, a daya bangaren, muna iya cewa mun shiga sabuwar shekarar ta bana da kyakkyawan fatan kyautatuwar lamura, musamman ganin yadda salon diflomasiyyar kasar Sin ke kara samar da tagomashi ga cundayar al’ummun duniya bisa mutunta juna, da yunkurin kare moriyar juna, da adawa da matakan kashin kai, ko keta hurumin ’yancin kasashe na mulkin kai da kiyaye yankunansu.

Mun ga yadda manyan jami’an Sin suka bude shekarar da ziyartar kasashen ketare da dama, domin sada zumunta, da kara yaukaka fahimtar juna, ciki har da ziyarar da ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya kai kasashen Habasha, da Tanzania da Lesotho dake nahiyar Afirka. Ziyarar da ta kasance karo na 36 a jere da ministan wajen kasar Sin ke zuwa kasashen Afirka a duk farkon shekara. Ta kuma zo a gabar da ake cika shekaru 70 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da kasashen Afirka.

Masharhanta na cewa, wannan ziyara ta alamta yadda kasar Sin ta dukufa wajen zurfafa kawance bisa adalci, da daidaito, da martaba juna, da burin cimma moriya tare. Ta hanyar aiwatar da matakai na zahiri, kasar Sin ta ci gaba da ingiza daidaito, da karsashi ga ci gaban duniya duk da tarin kalubale da ake fama da su.

ADVERTISEMENT

A kurkusa ma, kasar Sin na kara kyautata cudanya, da zumunci tare da makwaftanta, kamar dai yadda muka ga kokarin kasar na zurfafa tattaunawa da kasashe irin su Pakistan, da Koriya ta kudu, da nufin haifar da karin daidaiton alakar makwaftaka, da aminci da bunkasa hadin gwiwa.

Har ila yau, yayin da kasashe da dama ke shan radadin karin harajin fito daga matakan kasar Amurka, a nata bangare kasar Sin ta bullo da manufar janye daukacin harajin kwastam kan hajojin dake shiga kasar daga kasashen Afirka dake da huldar diflomasiyya tare da ita, wanda hakan ke kara shaida kwazon kasar Sin na tallafawa, da goyon bayan muradun kasashe masu tasowa na samun ci gaba cikin lumana.

LABARAI MASU NASABA

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

Yayin da ake ganin yunkurin wasu manyan kasashen duniya na kafa tsarin danniya da babakere, da kulla kawancen mayar da wasu sassa saniyar ware, a nata bangare kuwa, kasar Sin ta dukufa ne wajen shawo kan kalubalolinta na cikin gida, da kuma raba damammakin ci gabanta mai inganci ga sauran sassan kasa da kasa, karkashin salon diflomasiyyar ta dake cike da fatan cimma nasara cikin lumana, da gina al’ummar duniya mai makomar bai daya ga dukkanin bil’adama. Salon diflomasiyyar da ke shan jinjinawa da goyon baya daga dukkanin kasashe masu fatan a “gudu tare a tsira tare”!(Saminu Alhassan)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin
  • Sulaiman
    An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • Sulaiman
    Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin
  • Sulaiman
    Shugaban Mongoliya Ya Zanta Da Ministan Wajen Kasar Sin

MASU ALAKA

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026
An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
Daga Birnin Sin

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 14, 2026
Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin
Daga Birnin Sin

Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

June 14, 2026
Next Post
EFCC Ta Gabatar Da Ƙarin Hujjoji A Shari’ar Tsohon Gwamnan Kogi, Yahaya Bello

EFCC Ta Gabatar Da Ƙarin Hujjoji A Shari’ar Tsohon Gwamnan Kogi, Yahaya Bello

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

June 15, 2026
An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

June 14, 2026
Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

June 14, 2026
An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 14, 2026
Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

June 14, 2026
Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.