Shugaban Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Ƙasa NPA, Dakta Abubakar Ɗantsoho, ya jinjina wa Hukumar daidaiton rabon muƙamai ta ƙasa wato, FCC, kan sabbin sauye-sauyen da take ci gaba da ƙirƙirowa.
Ya ce, sauye-sauyen, sun kuma zo daidai da ƙoƙarin da Gwamnatin Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ke ci gaba da yi, na sabunta hukumomin Gwamnatin Tarayya.
Ɗantsho ya kuma bai wa Hukumar tabbacin cewa, za ta ci gaba da yin biyaya da ɗaukacin dokokin Hukumar ta FCC.
Ɗantsoho ya sanar da haka ne, a ranar Juma’a yayin tattanawa da mahukuntan Hukumar NPA da kwamtin ayyuka da na kula da zirga-zirga da na sufurin Jiragen sama na Hukumar ta FCC.
Tattaunawar ta gudana ne, a shalkwatar Hukumar ta FCC da ke Abuja.
Shugaban na NPA, ya bayyana gamsuwarsa, kan wannan tataunawar tare da tarbar ban girma da mahukuntan Hukumar ta FCC suka yiwa tawagarsa.
Ya yi nuni da cewa, tattaunawar ta nuna a zahiri, kan irin mayar da hankali da aka yi, wajen gudanar da duk wasu ayyka, bias tafarkin yin gaskiya da bin ƙa’aida.
“Ina danganta wannan nasarorin da ake kan ci gaba da samarwa, kan ƙoƙarin da Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ke gaba da yi, musamman wajen ƙara haɓaka fannin sufurin Ɗantsoho,”.
Kazalika, ya nanata cewa, haɗaka a tsakanin Hukumomin Gwamnati, zai ƙara ciyar da Nijeriya gaba, haka kuma bin ƙa’idoji da tsare-tsaren da dokokin da Gwamnatin ta shinfiɗa, za su ƙara ƙarfafa ƙara gudanar da ayyuakn Gwamnatin, yadda ya kamata.
Ɗantsoho yayi nuni da cewa, wannan haɗakar a tsakanin NPA da FCC, za ta taiamaka matuƙa, wajen ƙara gudanar da shugabanci da kuma tallawa ƙara ciyar da Nijeriya gaba.
Ya sanar da cewa, shekaru da dama da suka gabata, NPA ta ci gaba da kasancewa, kan gaba wajen bayar da gagarumar gudunmawa, na ƙara ciyar da ƙasar gaba.
Shugaban ya ce, a baya Rundunar Sojin Ruwan ƙasar nan, da Hukumar Hukumar Kula da Harkokin Tsaron Tashoshin Jiragen Ruwa ta Ƙasa wato NIMASA, sun kasance suna haɗe ne da NPA, kafin a raba su.
A cewrasa, NPA ce har yau, ke ci gaba da kula da ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa na Fatakwal, Warri, Calabar, Onne, Tin Can Island, Apapa da Lekki, musamman duba da nauyin da aka ɗora mata na tabbatar da shiga da fitar Jiragen Ruwa na ƙasa da ƙasa.
Ɗantsoho ya ƙara da cewa, Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya, na gudanar da ayyukansu ne, daidai na ƙasashen Cotonou, Lomé, Ghana da Abidjan, musamman wajen kula da saukar Jiragen Ruwa.
A na sa jawabin, Sugaban Kwamtin na FCC Honorabil Peter Eze, yabawa mahukuntan NPA, musamman kan haɗakar, inda ya ce, manufar wannan tattaunawar shi ne, domin a ƙara ƙarfafa haɗaka, a tsakanin hukumomin biyu, wajen ƙara tabbatar da ana gudnar da yin gaskiya wajen gudanar da ayyakan Gwamnatin Tarayya yadda ya kamata.
Ya kuma bayyana jin daɗinsa ƙarara, kan irin gudanar da shugabanci na gari na Dakta Ɗantsoho, musamman kan yadda yake ci gaba da mayar da hankali, wajen ƙara ciyar da NPA gaba.













