Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, zai ci gaba da kasancewa a hannun ICPC bayan da Babbar Kotun Jihar Kaduna ta dage sauraron buƙatar belinsa.
An fara tsare El-Rufai ne a kusa da ranar 19 ga Fabrairu, 2026, bayan da kotu ta ba hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa izinin tsare shi bisa zarge-zargen da suka shafi lokacin da yake gwamnan Jihar Kaduna. Daga bisani kuma an ƙara wa’adin tsare shi a ranar 5 ga Maris, 2026, yayin da ake cigaba da gudanar da bincike.
- Sin Na Da Burin Ganin Al’ummun Sin Da Na Amurka Sun Ingiza Ruhin Diflomasiyar Kwallon Tebur
- Xi Jinping: Matasa Ne Suka Kirkiro Dangantakar Sin Da Amurka
A zaman da ya gabata, lauyan ICPC ya shaida wa kotu cewa bincike bai kammala ba, inda ya nemi ƙarin lokaci domin kammala binciken, yana mai cewa bayar da beli a wannan mataki na iya kawo cikas ga aikin binciken.
Sai dai lauyoyin El-Rufai sun roƙi kotu da ta ba shi beli, suna masu jaddada cewa ya ba da cikakken haɗin kai ga masu bincike kuma ba shi da niyyar tserewa.
Bayan sauraron bangarorin biyu, kotu ta dage shari’ar zuwa ranar 21 ga Afrilu, 2026 domin ci gaba da sauraron ƙarar.
Tsohon gwamnan zai ci gaba da kasancewa a hannun ICPC har zuwa zaman na gaba, yayin da shari’ar ke ci gaba da jawo hankalin al’umma a faɗin ƙasa.















Discussion about this post