Fadar firaministan kasar Birtaniya ta sanar a ranar 11 ga wata cewa, kasar
za ta dakatar da shirin mika tsibiran Chagos ga Mauritius, sakamakon
rashin samun goyon baya daga shugaban kasar Amurka Donald Trump.
“Mun sha bayyana cewa, ba za mu aiwatar da shirin ba sai da goyon
bayan Amurka”, in ji gwamnatin Birtaniya. Lallai abun ban mamaki ne
cewa maido da yankin wata kasa mai mulkin kanta hannunta, sai da
amincewar wata kasa ta daban.
Tsibiran Chagos suna tekun Indiya da ke da nisan kilomita 750 daga
arewa maso gabashin kasar Mauritius. Bisa yarjejeniyar Paris, Birtaniya
ta kwace Mauritius da ma tsibiranta daga hannun Faransa a shekarar
1814, kuma daga nan ta fara mulkin mallaka na sama da shekaru 150 a
kasar. Ya zuwa shekarar 1965, Birtaniya ta tilasta wa Mauritius bayar da
tsibiran Chagos bisa sharadi na “ba ta ’yancin kai”. A shekarar 1966
kuma, Birtaniya ta daddale yarjejeniya tare da Amurka, inda ta ba da
hayar tsibirin Diego Garcia ga Amurka don ta gina sansanin sojojinta a
wurin, tsibirin da ya kasance mafi girma daga cikin tsibiran Chagos,
kuma domin gina sansanin, har an tilastawa mutane kimanin 2000 ’yan
asalin tsibirin barin muhallansu. Ma iya cewa tsibiran Chagos sun shaida
tarihin mulkin mallaka na yadda kasashen yamma suka yi abin da suka ga
dama ga wata kasar Afrika mai mulkin kai.
Mauritius ta dade tana ja-in-ja da Birtaniya game da batun ikon tsibiran
Chagos. A shekarar 2019, kotun kasa da kasa karkashin MDD ta yanke
hukuncin cewa, ya kamata Birtaniya ta maido da tsibiran Chagos ga
Mauritius. Daga nan kuma har zuwa watan Mayun shekarar 2025, aka kai
ga cimma yarjejeniyar maido da tsibiran a tsakanin kasashen biyu. Sai dai
bisa yarjejeniyar, dole ne Mauritius ta ci gaba da ba da hayar tsibirin
Diego Garcia ga Birtaniya da kuma Amurka.
To, amma me ya sa Amurka ta ki yarda Birtaniyata ta mayar da tsibiran
Chagos hannun Mauritius? Dalilin shi ne sansanin soja da Amurka din ta
kafa a tsibirin Diego Garcia, wanda ke da matukar muhimmanci ga
Amurka. Tun bayan da aka fara aiki da sansanin, Amurka ta girke
nau’o’in jiragen saman kai hari a sansanin, don yin amfani da shi wajen
shawo kan mashigar tekun Hormuz da ta Bab El-Mandeb, har ma da
gabar tekun Aden da ke kusa da tsibirin. Musamman ta yin la’akari da
yanayin rikicin da ka iya kara tabarbarewa a tsakanin Amurka da Iran,
Amurka na bukatar tsibirin wajen shawo kan Iran da yankin gabas ta
tsakiya.
A hakika, abin da ya faru ga tsibiran Chagos ya tono mana ainihin
yanayin kasashen yamma na nuna fin karfi, baya ga nuna wahalhalun da
ake fuskanta wajen kawar da mulkin mallaka daga fadin duniya. Duk da
haka, hannun agogon tarihi ba zai koma baya ba, saboda wani shingen danniya na dan lokaci.
A cikin ’yan shekarun baya, har kullum kungiyar tarayyar Afirka na mai
da hankalinta a kan batun tsibiran Chagos, kuma a ganinta, yadda
Birtaniya ta balle tsibiran daga yankin Mauritius ya saba wa kudurori da
dama na MDD, kuma batun a maimakon a ce takaddama ce tsakanin
Birtaniya da Mauritius, batu ne mai muhimmanci kan ko za a kai ga
kawar da mulkin mallaka kwata-kwata daga nahiyar Afirka ko a’a. Sai
kuma a game da matakan da Birtaniya da Amurka suka dauka, Dhananjay
Ramful, ministan kula da harkokin waje, da dunkulewar shiyya, da
cinikayyar kasa da kasa na Mauritius, ya ce kasarsa za ta yi iyakacin
kokarin kawar da mulkin mallaka daga shiyyar ta hanyoyin diplomasiyya
da kuma na shari’a.
Kawar da mulkin mallaka daga fadin duniya abu ne da ba za a iya hana
shi ba, duk da matsalolin da ake iya fuskanta, amma tabbas za a ga
bayansa. Kamar dai yadda masani kan ilimin tsarin mulkin duniya na
Nijeriya Livingstone Wechie ya ce, lokaci ya wuce da za a bari kasashen
yamma, ta fakewa da duk wani dalili su rika cin zalin wani bangare na
kasashe masu tasowa.















Discussion about this post