ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping: Matasa Ne Suka Kirkiro Dangantakar Sin Da Amurka

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
Amurka

A jiya Lahadi aka kammala rangadi na shirin musayar al’adu da kimiyya da fasaha na matasan Amurka na bana a birnin Chongqing na kasar Sin, wanda ya samu halartar dalibai da malamai 106 daga jami’o’i sama da 20 na Amurka.

Rangadin ya kushi ziyarce-ziyarce a jami’o’i da cibiyoyin bincike na kimiyya da fasaha da wuraren tarihi da sauransu, wanda ke nufin dalibai da malamai ’yan asalin Amurka 106 sun ganewa idanunsu kasar Sin tare da fahimtar al’adu da ci gaban kasar.

Shin mene ne fa’idar irin wannan ziyara?

ADVERTISEMENT

A matsayinsu na kasashe masu karfin tattalin arziki da ma karfin fada a ji a duniya, kowa ya san irin alfanun da za a samu daga kyautatuwar dangantaka tsakanin Sin da Amurka, domin ba su kadai da al’ummominsu ne za su amfana ba, har da sauran sassan duniya.

A baya-bayan nan, shugaban kasar Sin ya aike da wani sakon taya murna albarkacin cika shekaru 55 da kulluwar diplomasiyya tsakanin kasar Sin da Amurka daga wasan Kwallon Tebur watau Ping-Pong Diplomacy, wadda ta share fagen dangantakar kasashen biyu, inda ya ce, “jama’a ne suka gina tushen dangantakar Sin da Amurka, kana matasa ne suka kirkiro makomarta.” Tabbas matasa suna da rawar takawa wajen inganta dangantaka tsakanin kasa da kasa, musamman irin dangantakar da ke tsakanin Sin da Amurka da a kullum ake samun masu neman shafawa Sin bakin fenti da yada karairayi.

LABARAI MASU NASABA

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

Hausawa na cewa, gani ya kori ji. Irin wannan musaya za ta taka rawa matuka gaya wajen kyautata fahimtar juna da rage kyama ko wariya da kuma gina alaka mai dorewa tsakanin al’ummomin kasashen. Idan matasa suka hadu, suka yi mu’amala tare, to ba makawa za a samu fahimtar al’adun juna wanda ya zarce ra’ayi na siyasa da suke dauke da shi, haka kuma dama ce ta koyi da juna. Wannan mu’amala ce za ta gina tubalin aminci da abota da saukaka duk wani sabani da ke akwai.

Baya ga haka, dama ce ta musayar ra’ayi a ilimance, lamarin da zai haifar da ingantattun kirkire-kirkire da ci gaba ga duniya baki daya. Mu’amala tsakanin matasa tamkar shuka iri ne da zai girma a ci moriyarsa a nan gaba. Hakika Sin ta yi hangen nesa, na bude kofofinta ga matasan Amurka, domin ba su damar fahimtar kasar da samun ra’ayi na kashin kansu maimakon abun da suke ji da gani a kafafen yada labarai, inda wannan ra’ayi ba zai tsaya a zukatansu ba, domin za su yayata abun da suka gani ga sauran ’yan uwansu da abokan arziki. Fatan ita ce matasan bangarorin biyu su ci gaba da kirkiro kyakkyawar makomar dangantakar kasashen biyu domin gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya ta Sin da Amurka. (Fa’iza Mustapha)

Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana
  • Sulaiman
    Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya
  • Sulaiman
    Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa
  • Sulaiman
    Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

MASU ALAKA

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

June 7, 2026
Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya
Daga Birnin Sin

Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

June 7, 2026
Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

June 7, 2026
Next Post
Babu Shirin Hana Jam’iyyun Adawa Shiga Zaɓen 2027 – Fadar Shugaban Ƙasa

Babu Shirin Hana Jam’iyyun Adawa Shiga Zaɓen 2027 – Fadar Shugaban Ƙasa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

June 8, 2026
Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

June 8, 2026
Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

June 8, 2026
An Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram, Wasu Na Can Riƙe Wurinsu

An Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram, Wasu Na Can Riƙe Wurinsu

June 8, 2026
Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

June 7, 2026
A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

June 7, 2026
An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

June 7, 2026
Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

June 7, 2026
NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

June 7, 2026
Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

June 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.