ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping: Matasa Ne Suka Kirkiro Dangantakar Sin Da Amurka

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
Amurka

A jiya Lahadi aka kammala rangadi na shirin musayar al’adu da kimiyya da fasaha na matasan Amurka na bana a birnin Chongqing na kasar Sin, wanda ya samu halartar dalibai da malamai 106 daga jami’o’i sama da 20 na Amurka.

Rangadin ya kushi ziyarce-ziyarce a jami’o’i da cibiyoyin bincike na kimiyya da fasaha da wuraren tarihi da sauransu, wanda ke nufin dalibai da malamai ’yan asalin Amurka 106 sun ganewa idanunsu kasar Sin tare da fahimtar al’adu da ci gaban kasar.

Shin mene ne fa’idar irin wannan ziyara?

ADVERTISEMENT

A matsayinsu na kasashe masu karfin tattalin arziki da ma karfin fada a ji a duniya, kowa ya san irin alfanun da za a samu daga kyautatuwar dangantaka tsakanin Sin da Amurka, domin ba su kadai da al’ummominsu ne za su amfana ba, har da sauran sassan duniya.

A baya-bayan nan, shugaban kasar Sin ya aike da wani sakon taya murna albarkacin cika shekaru 55 da kulluwar diplomasiyya tsakanin kasar Sin da Amurka daga wasan Kwallon Tebur watau Ping-Pong Diplomacy, wadda ta share fagen dangantakar kasashen biyu, inda ya ce, “jama’a ne suka gina tushen dangantakar Sin da Amurka, kana matasa ne suka kirkiro makomarta.” Tabbas matasa suna da rawar takawa wajen inganta dangantaka tsakanin kasa da kasa, musamman irin dangantakar da ke tsakanin Sin da Amurka da a kullum ake samun masu neman shafawa Sin bakin fenti da yada karairayi.

LABARAI MASU NASABA

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya

Hausawa na cewa, gani ya kori ji. Irin wannan musaya za ta taka rawa matuka gaya wajen kyautata fahimtar juna da rage kyama ko wariya da kuma gina alaka mai dorewa tsakanin al’ummomin kasashen. Idan matasa suka hadu, suka yi mu’amala tare, to ba makawa za a samu fahimtar al’adun juna wanda ya zarce ra’ayi na siyasa da suke dauke da shi, haka kuma dama ce ta koyi da juna. Wannan mu’amala ce za ta gina tubalin aminci da abota da saukaka duk wani sabani da ke akwai.

Baya ga haka, dama ce ta musayar ra’ayi a ilimance, lamarin da zai haifar da ingantattun kirkire-kirkire da ci gaba ga duniya baki daya. Mu’amala tsakanin matasa tamkar shuka iri ne da zai girma a ci moriyarsa a nan gaba. Hakika Sin ta yi hangen nesa, na bude kofofinta ga matasan Amurka, domin ba su damar fahimtar kasar da samun ra’ayi na kashin kansu maimakon abun da suke ji da gani a kafafen yada labarai, inda wannan ra’ayi ba zai tsaya a zukatansu ba, domin za su yayata abun da suka gani ga sauran ’yan uwansu da abokan arziki. Fatan ita ce matasan bangarorin biyu su ci gaba da kirkiro kyakkyawar makomar dangantakar kasashen biyu domin gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya ta Sin da Amurka. (Fa’iza Mustapha)

Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki
  • Sulaiman
    Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

MASU ALAKA

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 27, 2026
Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya
Daga Birnin Sin

Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya

June 27, 2026
Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

June 27, 2026
Next Post
Babu Shirin Hana Jam’iyyun Adawa Shiga Zaɓen 2027 – Fadar Shugaban Ƙasa

Babu Shirin Hana Jam’iyyun Adawa Shiga Zaɓen 2027 – Fadar Shugaban Ƙasa

LABARAI MASU NASABA

Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

June 28, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

El-Rufai Ya Shafe Fiye Da Kwanaki 125 A Garƙame

June 28, 2026
Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

June 28, 2026
Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

June 27, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Jaddada Cewa Ba Ta Da Wani Shiri Na Bada Damar Binciken Wuraren Nukiliyarta

June 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 27, 2026
Yaushe Za A Gane Kungiyar Da Za Ta Lashe Gasar Premier?

An Raba Jadawalin Gasar Premier Ta Ingila Ta Kakar Wasan 2026/2027

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.