ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping: Matasa Ne Suka Kirkiro Dangantakar Sin Da Amurka

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
Amurka

A jiya Lahadi aka kammala rangadi na shirin musayar al’adu da kimiyya da fasaha na matasan Amurka na bana a birnin Chongqing na kasar Sin, wanda ya samu halartar dalibai da malamai 106 daga jami’o’i sama da 20 na Amurka.

Rangadin ya kushi ziyarce-ziyarce a jami’o’i da cibiyoyin bincike na kimiyya da fasaha da wuraren tarihi da sauransu, wanda ke nufin dalibai da malamai ’yan asalin Amurka 106 sun ganewa idanunsu kasar Sin tare da fahimtar al’adu da ci gaban kasar.

Shin mene ne fa’idar irin wannan ziyara?

ADVERTISEMENT

A matsayinsu na kasashe masu karfin tattalin arziki da ma karfin fada a ji a duniya, kowa ya san irin alfanun da za a samu daga kyautatuwar dangantaka tsakanin Sin da Amurka, domin ba su kadai da al’ummominsu ne za su amfana ba, har da sauran sassan duniya.

A baya-bayan nan, shugaban kasar Sin ya aike da wani sakon taya murna albarkacin cika shekaru 55 da kulluwar diplomasiyya tsakanin kasar Sin da Amurka daga wasan Kwallon Tebur watau Ping-Pong Diplomacy, wadda ta share fagen dangantakar kasashen biyu, inda ya ce, “jama’a ne suka gina tushen dangantakar Sin da Amurka, kana matasa ne suka kirkiro makomarta.” Tabbas matasa suna da rawar takawa wajen inganta dangantaka tsakanin kasa da kasa, musamman irin dangantakar da ke tsakanin Sin da Amurka da a kullum ake samun masu neman shafawa Sin bakin fenti da yada karairayi.

LABARAI MASU NASABA

Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa

Manufar Sin Ta Ba Da Jagoranci Ga Tafiyar Da Fasahar AI A Duniya

Hausawa na cewa, gani ya kori ji. Irin wannan musaya za ta taka rawa matuka gaya wajen kyautata fahimtar juna da rage kyama ko wariya da kuma gina alaka mai dorewa tsakanin al’ummomin kasashen. Idan matasa suka hadu, suka yi mu’amala tare, to ba makawa za a samu fahimtar al’adun juna wanda ya zarce ra’ayi na siyasa da suke dauke da shi, haka kuma dama ce ta koyi da juna. Wannan mu’amala ce za ta gina tubalin aminci da abota da saukaka duk wani sabani da ke akwai.

Baya ga haka, dama ce ta musayar ra’ayi a ilimance, lamarin da zai haifar da ingantattun kirkire-kirkire da ci gaba ga duniya baki daya. Mu’amala tsakanin matasa tamkar shuka iri ne da zai girma a ci moriyarsa a nan gaba. Hakika Sin ta yi hangen nesa, na bude kofofinta ga matasan Amurka, domin ba su damar fahimtar kasar da samun ra’ayi na kashin kansu maimakon abun da suke ji da gani a kafafen yada labarai, inda wannan ra’ayi ba zai tsaya a zukatansu ba, domin za su yayata abun da suka gani ga sauran ’yan uwansu da abokan arziki. Fatan ita ce matasan bangarorin biyu su ci gaba da kirkiro kyakkyawar makomar dangantakar kasashen biyu domin gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya ta Sin da Amurka. (Fa’iza Mustapha)

Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Manufar Sin Ta Ba Da Jagoranci Ga Tafiyar Da Fasahar AI A Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    CDC Ta Afirka Ta Yaba Wa Sin Bisa Goyon Bayanta Ga Dakile Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Bukaci A Gudanar Da Aikin Ceto A Tsanake Bayan Rugujewar Bangaren Wani Tsauni A Chongqing
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa
  • Sulaiman
    Manufar Sin Ta Ba Da Jagoranci Ga Tafiyar Da Fasahar AI A Duniya
  • Sulaiman
    CDC Ta Afirka Ta Yaba Wa Sin Bisa Goyon Bayanta Ga Dakile Cutar Ebola
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Bukaci A Gudanar Da Aikin Ceto A Tsanake Bayan Rugujewar Bangaren Wani Tsauni A Chongqing

MASU ALAKA

Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa
Daga Birnin Sin

Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa

July 18, 2026
Manufar Sin Ta Ba Da Jagoranci Ga Tafiyar Da Fasahar AI A Duniya
Daga Birnin Sin

Manufar Sin Ta Ba Da Jagoranci Ga Tafiyar Da Fasahar AI A Duniya

July 18, 2026
CDC Ta Afirka Ta Yaba Wa Sin Bisa Goyon Bayanta Ga Dakile Cutar Ebola
Daga Birnin Sin

CDC Ta Afirka Ta Yaba Wa Sin Bisa Goyon Bayanta Ga Dakile Cutar Ebola

July 18, 2026
Next Post
Babu Shirin Hana Jam’iyyun Adawa Shiga Zaɓen 2027 – Fadar Shugaban Ƙasa

Babu Shirin Hana Jam’iyyun Adawa Shiga Zaɓen 2027 – Fadar Shugaban Ƙasa

LABARAI MASU NASABA

Burina Zama Daya Daga Cikin Fitattun Masu Daukar Hoto A Nijeriya –Ibrahim Aminu

Burina Zama Daya Daga Cikin Fitattun Masu Daukar Hoto A Nijeriya –Ibrahim Aminu

July 18, 2026
Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa

Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa

July 18, 2026
Manufar Sin Ta Ba Da Jagoranci Ga Tafiyar Da Fasahar AI A Duniya

Manufar Sin Ta Ba Da Jagoranci Ga Tafiyar Da Fasahar AI A Duniya

July 18, 2026
CDC Ta Afirka Ta Yaba Wa Sin Bisa Goyon Bayanta Ga Dakile Cutar Ebola

CDC Ta Afirka Ta Yaba Wa Sin Bisa Goyon Bayanta Ga Dakile Cutar Ebola

July 18, 2026
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaduwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaduwa Tsakanin Ma’aurauta

July 18, 2026
Xi Jinping Ya Bukaci A Gudanar Da Aikin Ceto A Tsanake Bayan Rugujewar Bangaren Wani Tsauni A Chongqing

Xi Jinping Ya Bukaci A Gudanar Da Aikin Ceto A Tsanake Bayan Rugujewar Bangaren Wani Tsauni A Chongqing

July 18, 2026
Yadda Ake Miyar Karkashi Da Nama

Yadda Ake Miyar Karkashi Da Nama

July 18, 2026
Kura-kurai 7 Da Mata Ke Yi Wajen Kula Da Fatarsu

Kura-kurai 7 Da Mata Ke Yi Wajen Kula Da Fatarsu

July 18, 2026
Majalisa Ta Goyi Bayan CBN Kan Sauya Fasalin Naira Bayan Tafka Muhawara 

Majalisa Ta Yi Watsi Da Bukatar MDD Ta Bincikar Badakalar Satar Daliban Oyo

July 18, 2026
Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

July 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.