A jiya Lahadi aka kammala rangadi na shirin musayar al’adu da kimiyya da fasaha na matasan Amurka na bana a birnin Chongqing na kasar Sin, wanda ya samu halartar dalibai da malamai 106 daga jami’o’i sama da 20 na Amurka.
Rangadin ya kushi ziyarce-ziyarce a jami’o’i da cibiyoyin bincike na kimiyya da fasaha da wuraren tarihi da sauransu, wanda ke nufin dalibai da malamai ’yan asalin Amurka 106 sun ganewa idanunsu kasar Sin tare da fahimtar al’adu da ci gaban kasar.
Shin mene ne fa’idar irin wannan ziyara?
A matsayinsu na kasashe masu karfin tattalin arziki da ma karfin fada a ji a duniya, kowa ya san irin alfanun da za a samu daga kyautatuwar dangantaka tsakanin Sin da Amurka, domin ba su kadai da al’ummominsu ne za su amfana ba, har da sauran sassan duniya.
A baya-bayan nan, shugaban kasar Sin ya aike da wani sakon taya murna albarkacin cika shekaru 55 da kulluwar diplomasiyya tsakanin kasar Sin da Amurka daga wasan Kwallon Tebur watau Ping-Pong Diplomacy, wadda ta share fagen dangantakar kasashen biyu, inda ya ce, “jama’a ne suka gina tushen dangantakar Sin da Amurka, kana matasa ne suka kirkiro makomarta.” Tabbas matasa suna da rawar takawa wajen inganta dangantaka tsakanin kasa da kasa, musamman irin dangantakar da ke tsakanin Sin da Amurka da a kullum ake samun masu neman shafawa Sin bakin fenti da yada karairayi.
Hausawa na cewa, gani ya kori ji. Irin wannan musaya za ta taka rawa matuka gaya wajen kyautata fahimtar juna da rage kyama ko wariya da kuma gina alaka mai dorewa tsakanin al’ummomin kasashen. Idan matasa suka hadu, suka yi mu’amala tare, to ba makawa za a samu fahimtar al’adun juna wanda ya zarce ra’ayi na siyasa da suke dauke da shi, haka kuma dama ce ta koyi da juna. Wannan mu’amala ce za ta gina tubalin aminci da abota da saukaka duk wani sabani da ke akwai.
Baya ga haka, dama ce ta musayar ra’ayi a ilimance, lamarin da zai haifar da ingantattun kirkire-kirkire da ci gaba ga duniya baki daya. Mu’amala tsakanin matasa tamkar shuka iri ne da zai girma a ci moriyarsa a nan gaba. Hakika Sin ta yi hangen nesa, na bude kofofinta ga matasan Amurka, domin ba su damar fahimtar kasar da samun ra’ayi na kashin kansu maimakon abun da suke ji da gani a kafafen yada labarai, inda wannan ra’ayi ba zai tsaya a zukatansu ba, domin za su yayata abun da suka gani ga sauran ’yan uwansu da abokan arziki. Fatan ita ce matasan bangarorin biyu su ci gaba da kirkiro kyakkyawar makomar dangantakar kasashen biyu domin gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya ta Sin da Amurka. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post