Tsohon gwamnan Jihar Anambra kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP a zaɓen 2023, Peter Obi, ya sake jaddada aniyarsa ta yin wa’adi guda ɗaya na shekaru huɗu kacal idan aka zaɓe shi shugaban ƙasa a 2027.
Obi ya bayyana hakan ne a wata hira da gidan TV na News Central a ranar Alhamis, inda ya ce ba zai ci gaba da zama a mulki fiye da wa’adi ɗaya ba a kowane irin hali.
“Ina son zama shugaban ƙasa na wa’adi ɗaya ne saboda kwanciyar hankali. Ba zan ƙara kwana guda bayan shekaru huɗu ba, ko da an ɗora min bindiga a kai,” in ji Obi.
Rahotanni sun nuna cewa Obi da tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, sun fice daga jam’iyyar ADC zuwa jam’iyyar NDC a ranar 3 ga Mayu.
Bayan kwanaki kaɗan, a ranar 9 ga Mayu, jam’iyyar NDC ta sanar da cewa za ta bai wa yankin Kudancin Nijeriya tikitin takarar shugaban ƙasa na zaɓen 2027, yankin da Obi ya fito.















Discussion about this post